Cibiyar dake dakile cututtuka masu yaduwa ta Nijeriya, NCDC a daren jiya Alhamis ta wallafa cewa Nijeriya ya zuwa daren jiya masu dauke da cutar Korona sun doshi mutum dubu goma sha biyu.
Inda a jiya Alhamis kawai an samu mutum 350 da suke dauke da cutar ta Korona daga wadansu jihohin kasar. Wanda hakan ya sanya yanzu mutum 11,516 ke dauke da cutar.
NCDC sun tabbatar da cewa sabbin masu dauke da Korona din sun fito ne daga jihohin Legas (102), Ogun (34), FCT (29), Borno (26), Kaduna (23), Rivers (21), Kwara (16), Ebonyi (17), Katsina (14), Edo (10), Delta (10), Kano (10), Bauchi (10), Bayelsa (9), Imo (8), Plateau (4), Ondo (3), Nasarawa (2), Gombe (1) da Oyo (1).
Babu wata sabuwar jiha dai da cutar ta bulla cikin awa 24. Sai dai ya zuwa yanzu mutum 7,658 kawai ake duba lafiyarsu, yayin tuni aka salami mutum 3,535, inda kuma 323 suka rasa rayukansu cikin jihohi 35 ciki kuwa harda birnin tarayya Abuja.