Fadar shugaban kasa ta bayyana cewa wasu daga cikin masu sarautun gargajiya dake jihar Katsina ne daukar nauyin ta’addancin ‘yan bindiga da ake yi a jihar shugaban kasa Manjo Jabar Muhammad Buhari.
Hakan ya fito ne daga bakin mai magana da yawun shugaban kasa Malam Garbage Shehu, a yayin wata tattaunawa da aka yi da shi a cikin shirin ‘Sunrise’ na gidan Talabijin din ‘Channels’ a safiyar yau.
Ya ce “ba Wai muna son dorawa kowa kazafi bane, amma an samu masu sauratun gargajiya a mahaifar shugaban kasa suna daukar nauyin cutar al’ummarsu”.
“A zamfara kusa wadda take makwabtaka da Katsina an samu dagatai da hakimai Wanda aka tube su saboda Kama su da aka yi da hada kai da ‘yan ta’adda”.
https://dimokuradiyya.com.ng/mazauna-garin-yantumaki-dake-jihar-katsina-sun-yi-zanga-zanga/
Shehu ya kara da cewa, ‘yan bindigar ana Basu rahotannin a duk lokacin da sojin kasar nan suke kokarin kai musu bari, Wannan yana nuni da cewa akwai mazabamta a tafiyar.
Hadimin ya kara da cewa wasu daga cikin al’ummar kasar nan na ganin Kamar shugaban Buhari na da maganin dukkanin matsalolin da kasar nan ke fustanka, amma yace Wannan aiki bana shugaban kasa kadai bane aiki ne na kowa da kowa.
Idan ba a manta ba a ‘yan kwanakin da suka gabata ne aka gudanar da zanga-zanga a wasu yankuna na jihar Katsina inda har wasu suka kona all on tallan hoton Bihari da Gwamna Masari, inda masu zanga-zangar ke ganin cewa shuwagabannin sun kasa magance mush matsalarsu.