• Ya kamata masu yabo su san irin kalaman da suke yi lokacin yin yabo.
• “Bai kamata a ce Mai yabon Annabi Yana amfani da kalmomi masu harshen da bo ba” inji ta.
• Yabon Annabi idan anbi tsarin shari’a abune mai kyau.
Daga Mukhtar Yakubu Kano.
An yi kira ga masu Yabon Annabi S A W, da su rinka kiyaye kalmomin da za su rinka furtawa, wajen yabon da su ke yi wa Manson Allah S A W.
Wannan bayanin ya fito ne daga bakin daya daga cikin Sha’irai mata da su ke harkar yabon Manzon Allah S A W, wato Maimuna Ibrahim, wacce aka fi sani da sunan Ummee Burdatu a lokacin da su ke tattaunawa da wakilin jaridar Dimokuradiyya a Kano, dangane da yadda mata su ke shigowa cikin harkar yabon Manzon Allah S A W a wannan lokacin.
KARANTA WANNAN LABARIN: Sanata Peter ya koma Jam’iyar APC
Sha’irar ta bayyana cewar “Yabon da mata su ke yana da kyau su rinka tsarkake harshen su, wajen furuci a wakokin da su ke yi.”
Ta Kara da cewar” Babban buri na a yanzu, na ga an sai ta hanya a yabo an gyara kurakurai, musamman na furuci da kalmomi, don akwai furucin da bai kamata a yi wa Ma’aiki ba, saboda ba su cancanta a saka su a sahun yabo ba, kamar kalma mai harshen Damo, ba a saka ta a bege, don tana bayar da ma’ana bayu, sai ya zama kai mai yabon har zuciyarka mai kyau din ka dauka, shi kuma mai sauraro sai ya dauke ta a marar kyau, ka ga wannan abin shi ne ya ke hada jayayya, don haka, ina kira ba Sha’irai da su rinka tsarkake niyyar su, da kuma bakin su a wajen yabon Manzon Allah S A W, domin kuwa harkar yabo tana da muhimanci idan har an yi ta yadda take cikin tsari. ”
Dangane da yadda mata su ke shiga kuwa a wajen Majalisi, nan ma ta yi kira ga mata, da su rinka saka suturar da za ta rufe musu jikin su, domin bai kamata mata su rinka zuwa wajen Majalisi da shigar da ba ta dace ba, don haka mata Sha’irai a rinka kiyaye mutunci idan za a tafi wajen Majalisi.”
Daga karshe ta yi fatan samun dacewa da soyayyar Manzon Allah S A W, wanda da man muna yi ne, domin samun soyayyar sa. In ji Ummee Burdatu.
Comments 1