Mataimakin Shugaban kasa, Yemi Osinbajo a jiya Alhamis, 30 ga watan Mayu ya bayyana limamin addinin Musulunci dan shekara 83, Imam Abdullahi Abubakar, wanda ya ceci Kiristoci 300 daga hallaka a jihar Filato a matsayin jarumi, wanda ya cancanci karramawa.
Limamin ya cece su ne ta hanyar boye su a cikin masallaci lokacin da wasu yan bindiga suka kai farmaki Yelwan Gindi Akwati, kauyukan Swei da Nghar a karamar hukumar Barkin Ladi da ke jihar Filato, a shekarar da ya gabata.
Osinbajo ya kwararo ruwan yabo ga malamin a fadar Shugaban kasa, Abuja, lokacin da ya karbi bakuncinsa; da na sarkin kauyen Damafulul Mangai, sauran shugabannin garuruwa da wata tawaga da ta hada da yan diflomaasiyya daga Amurka, Ingila da kuma tarayyar turai.
Da yake bayyana abunda Abubakar yayi a matsayin jarumta, mataimakin Shugaban kasar ya bayyana cewa Imam ya yi namijin kokari domin ya wanzar da zaman lafiya ta hanyar abunda ya aikata fiye da wasu yan siyasa da dama don haka ya cancanci duk wani yabo da karramawa mafi girma.