Matasa a karamar hukumar Bakassi sun bukaci Gwamnatin tarayya data biya su kudin fansa a dalilin rasa garin Bakassi da suka yi da kuma rijiyoyin man fetur din su.
An rawaito wannan Labarin ne a wata budaddiyar wasika da Matasan karamar hukumar Bakassin suka rubutowa shugaban kasa Muhammadu Buhari, mai dauke da kwanan watan ranar 31 ga watan mayu 2019 mai suna letter of Demand, Wato wasikar bukata.
Matasan sun aika da wasikar zuwa ga hukumar yada labarai ta Kasa wanda Take a garin Kalaba, Shugaban matasan Akpankaya, a karamar hukumar Bakassin Mr Kingsley Asuquo Edem, a madadin matasan shi ya sanya hannu a takardan.
Shugaban matasan yace tunda aka mayar da garin ya koma yankin Kamaru hade da rijiyoyin man su har guda 76 a shekara ta 2002 shi kenan suke cikin talauci.
Yace zaman kotun da aka yi a wancan lokacin da wanda aka yanke hukuncin cewa Bakassi Peninsula na cikin yankin Kamaru wai ba a yi musu Adalci ba, inji shi.
Yace dubban mutane na wannan yankin sun rasa sana’o’in su da hanyar cin abinci a dalilin wannan mayar da yankin na Bakassi zuwa Kamaru.
Yace yawancin mutanen yankin manoma ne da masu kamun kifi sannan akwai Ma’adanai
Dan haka yace suna bukatar gwamnatin tarayya da ta yi gaggawan biyan su kudaden Da suke Bukata domin rage musu radadin Talaucin da yankin ke fama da shi a dalilin raba su da garin su na ainihi.
Dan haka suna bukatar hukumar National Boundary commission, ta gaggauta biyan su diya nan ba da jimawa ba.
Wannan yasa Muka rubuta wannan wasikar dan neman hakkinmu daga gwamnatin tarayya. Kuma suna bukatar shugaba Muhammadu Buhari da ya duba wannan al’amarin.