Wata kungiya mai suna Coalition of the Arewa Youth Organisation, ta ce kusan nan ba da dadewa ba matasan Najeriya za su karbi ragamar shugabancin kasar nan.
Mista Isaac David, mukaddashin kodinetan kungiyar ne ya bayyana haka a lokacin da yake jawabi ga manema labarai ranar Litinin a Abuja.
David ya ce zaben da aka yi wa Mohammed Kadade mai shekaru 25 a matsayin shugaban matasa na jam’iyyar PDP na kasa ya nuna yadda matasan Najeriya ke shirin karbar ragamar mulkin kasar.
Ya ce fitowar Kadade a matsayin shugaban matasan jam’iyyar zai kara yawan matasa da dama a harkar siyasa, yana mai cewa zabensa zai kara zaburar da sauran matasa wajen kokarin neman mukaman shugabancin kasar nan.
“Har yanzu akwai fatan wata rana za ta zo da matasa za su karbi ragamar mulkin kasar nan a matakin koli. A bayyane yake cewa kuzari da haske na tunanin matasa suna aiki ne a matsayin mai ɗaukar wuta don ci gaban ƙasa.
“Kasashen da suke amfani da matasansu ta hanya mai kyau sun fi ci gaba. Matasa su ne amintattun zuriyar kowace al’umma.