Tsohon hadimin shugaban kasa karkashin mulkin Alhaji Shehu Shagari, Alhaji Tanko Yakasai ya yi karin haske game da matasan da aka kama zasu kudancin kasar nan, cewa ba almajirai bane.
Yakasai ya bayyana haka ne, a yayin da yake tattaunawa da jaridar Vanguard inda ya ce ” ya kamata a bincika sosai saboda ni a ganina wadannan basu yi kama da almajirai ba”.
Ya kara da cewa “ni ba abinda na gani face matasan cikin riguna masu kyau wanda almajirai basa irin wannan shigar. Kowa yasan yanda almajirai suke kuma da ka gansu zaka gane, dan haka wadannan wasu ne na daban ba almajirai ba”.
“Wannan ba komai bane face nuna tsana da kiyayya da wasu ke nunawa wani bangare na Najeriya”.
“Tun ina dan shekaru 28 nake bawa kasar nan gudunmawa wajen ganin an samu hadin kai”.
“Dan haka ba zan taba goyon bayan wani bangare ko kuma zama daya daga cikin wanda basa son hadin kan Najeriya ba”.
Daga: Abubakar Muhammad Usman