Matsalar Tsaro: Ƴan Bindiga sun hallaka wani mutum bayan sun karɓi Miliyan 10 kudin fansa — Wase
Mataimakin Shugaban Majalisar Wakilai na Najeriya Idris Wase ya bayyana cewar ƴan bindiga yanzu suna hallaka mutanen da suka kama, bayan sun ƙarbi miliyoyi kuɗin fansa a Jahar Filato.
Wase ya bayyana haka a ranar Laraba, a lokacin da yake maida jawabi akan wani ƙudiri da aka gabatar, na gaggawa da Solomon Muren ya gabatar a zauren Majalisar.
KARANTA WANNAN LABARIN: NASU, SSANU sun ƙara wa’adin Yajin Aiki da watanni biyu
Ya ƙara dacewa al’ummomi da dama ƴan bindiga sun kore su daga garuruwan su, tare da sace masu shanun su.
Wase ya yi nuni dacewar, yanzu dole ta sanya mutane suna kare ƙauyukan su. Yana mai cewa yanzu matsayar Majalisar da ƙudirorin ta ya zama labari.
“A yanzu, al’ummar mazaɓa ta, suna neman mafaka. Yanzu an kori ƙauyuka da dama. Na gabatar da ƙudirori akan wannan lamari. A mazaɓa ta da nake wakilta, da wuya kwanaki biyu su wuce ba tare sace mutum ba da karɓar kuɗin fansa daga ƴan ƙauye. Kuma kuɗin fansa baya ƙasa da Miliyan 10.
“Na rasa kimanin mutane biyar, sun yi garkuwa an biya su kudi, kuma sun kashe su.
Biyo bayan wannan Ƙudiri, Majalisar ta umarci Kwamitin ta akan Ƴan Sanda da Sojoji dasu gayyaci Sufeto Janar da Shugaban Sojoji.
Majalisar tayi kira ga Jami’an tsaro dasu ɗauki jami’ai da yawa domin magance matsalar tsaro dake fuskantar Najeriya.