Matsalar Tsaro: APC tayi ga Ƴan Najeriya dasu yiwa Buhari addu’a
Jam’iyya mai mulki ta APC tayi kira ga ƴan Najeriya dasu yiwa Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari addu’a akan matsalolin tsaro dake fuskantar Ƙasar.
KARANTA WANNAN LABARIN: Ganduje ya yiwa daurarru 90 afuwa, tare da basu kudin mota don komawa gida
A cikin sakon Sallah zuwa ga Musulmi a ranar Asabar, Sakataren Yaɗa Labaru na Jam’iyyar APC Barr Felix Morka yace ƴan Najeriya dole su sanya Najeriya farko a zuciyar su.
Jam’iyyar tace “muna kira ga Ƴan Najeriya dasu cigaba da goyon bayan Gwamnatin Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari domin magance matsalar tsaro, tare da cigaba jefa da duk wani yunƙuri na siyasantar da Matsalar Tsaro a Kasar.
“A wannan lokaci na Bikin Babbar Sallah, muna kira ga Musulmi dasu cigaba da addu’a domin samun zaman lafiya da tsaro a ƙasar, a yayinda gwamnatin APC ke cigaba da bada fifiko ga jindaɗin ƴan Najeriya.
“A wannan lokaci muna kira ga ƴan Najeriya dasu sanya Najeriya farko a dukkanin lamurran su. Ba zamu daina yakar wanda suke Son suga sun rabamu da hanyar tsana