Shugaban majalisar Dattawan Nijeriya, Ahmad Lawan, a ranar Laraba ya bayyana cewa Nijeriya na bukatar addu’a domin magance matsalolin da take fuskanta.
Ola Awoniyi, mai bai wa shugaban majalisar shawara kan kafofin watsa labarai shi ne aka jiyo yana cewa, shugaban majalisar wato Ahmad Lawan ya bayyana hakan ne a yayin da tawagar kiristoci ‘yan majalisa suka kai masa ziyara.
Ahmad Lawan ya ce; idan aka yi duba da yanayin da Nijeriya ta fada da kuma al’ummar kasar, “to muna da bukatar addu’a sosai.” In ji shi.
Ya kara da cewa; “A yau muna fuskantar matsalar tsaro. Muna da hukumomin tsaro da aka daura musu alhakin magance matsalar tsaro da tabbatar da zaman lafiya, akwai bukatar mu taya su da addu’a domin ganin sun yi nasara a aikin su.” in ji shi.
Ya ce ba batun a ba su makamai bane kawai, karfin Allah ya fi karfin makami. Ya ce yana da imanin cewa; duk wani mai addini zai ci gaba da yiwa wadannan hukumomin tsaro addu’a domin ganin sun kare ‘yan kasa daga matsalar tsaro.