Mai martaba Sarkin Katsina, Alhaji Abdulmumini Kabir Usman ya ce ya sha fada wa Shugaba Muhammadu ya rika kula da makiya da ke ciki da wajen gwamnatinsa.
Sarkin ya yi ikirarin cewa wadannan makiyan ne suke kokarin tarwatsa yankin arewa kamar yadda ya bayyana a yayin wata tattaunawarsa da jaridar Daily trust.
Ya yi wannan jawabin ne a ranar Laraba yayin da ya ke magana da tawagar gwamnatin tarayya karkashin jagorancin mai bawa shugaban kasa shawara a kan tsaro, Janar Babagana Monguna (mai ritaya).
Tawagar da ta hada da Sufeta Janar na ‘yan sanda, Mohammed Adamu, Shugaban hukumar farin kaya ta DSS, Yusuf Magaji Bichi da daraktan hukumar NIA, Ahmed Rufai sun ziyarci Katsina ne don yin jaje bisa kisan da ‘yan bindiga suka yi a baya bayan nan.
Tawagar ta kuma ziyarci jihar ne domin tabbatar musu da cewa gwamnati na iya kokarin ta wurin ganin ta magance kallubalen tsaro a jihar da wasu yankunan kasar.
Idan za a iya tunawa, Kakakin Shugaba Buhari, Garba Shehu a hirar da aka yi da shi a Channels Television a ranar Litinin ya yi ikirarin cewa wasu masu sarautar gargajiya a Katsina ne ke daukar nauyin ayyukan ‘yan bindigar.
Ya ce wasu masu sarautan da bai ambaci sunan su ba suna taimakawa ‘yan bindigar su tsere duk lokacin da jamian tsaro ke shirin kai musu hari.