Hukumar Sadarwa ta Kasa wato NCC ta ba da umarnin ga kafatanin kamfanin layukan sadarwan waya da suke sadarwar baki daya a jihar Zamfara.
Umarnin rufe layukan sadarwan ya fara aiki ne a daren Juma’a a wani, inda gwamnati ta ce ta yi hakan ne a wani mataki na ba wa hukumomin tsaro damar gudanar da aikinsu a Jihar Zamfara domin dawo da tsaro da zaman lafiya da ayyukan ’yan bindiga ke yi wa barazana.
Sanarwar da NCC ta fitar ta ce, “Ci gaban matsalar tsaro a jihar Zamfara ya sa dole a rufe layukan sadarwa gaba daya a fadin jihar daga yau Juma’a, 3 ga Satumba, 2021.
“Saboda haka ake umartar Globacom ya gaggauta rufe duk tashoshin sadarwa da suke a fadin jihar da ma wadanda ke jihohi masu makwabtaka da ita da za a iya amfani da su wurin sadarwa a cikin jihar.”
Sanarwar ta kara da cewa za a rufe layukan sadarwan ne na tsawon mako biyu a karon farko.
Umarnin rufe layukan sadarwa a Jihar Zamfara na zuwa ne kwana biyu baya. ’yan bindiga sun kai hari a wata makarantar sakandare da ke kauyen Kaya a Karamar Hukumar Maradun ta jihar, suka yi awon gaba da dalibai maza da mata sa da 70.