Hukumar ‘yan sanda a jihar Katsina ta tabbatar da mutuwar mutane shida a yayin harin ‘yan bindiga a kauyukan Kanawa da Kanga dake ƙaramar hukumar Danmusa a jihar ta Katsina.
Mai magana da yawun hukumar SP Gambo Isa ya tabbatarwa da jaridar The Nation faruwar lamarin inda yace mata biyu masu ciki sun jikkata a dalilin harin ‘yan bindigar.
Gambo yace ” ‘yan bindigar sun kai su 100 wanda suka kai wa kauyukan hari da misalin karfe 2 na dare inda suka kashe mutane 6, sannan suka raunta guda 5″.
“A yayin da muka yi kokarin far musu sun kashe mana jami’i guda daya a cibiyar mu ta Maidabino. Mun tura ƙarin jami’an tsaro yankin domin ganin mun dakile su”.
Kamar yadda ya bayyana matan masu cikin an garzaya dasu babban asibitin karamar hukumar ta Danmusa domin basu agajin gaggawa.
Kamar yadda jaridar DAILYNIGERIAN ta rawaito, a baya-bayan nan jihar ta Katsina ta shiga wani mawuyacin hali sakamakon hare-haren ‘yan bindigar, wanda yasa har shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya umarci shugabannin tsaron ƙasar nan da suka ƙarshen ayyukan ta’addanci a jihar da ma wasu jihohin arewacin ƙasar nan.