A wani mataki na tsaurara tsaro a Kudancin Kaduna, Kwamishinnan ‘yan sandan jihar Kaduna, Umar Muri ya umurci da a gaggauta kara dakaru na musamman zuwa kananan hukumomin Kajuru, Zango Kataf, Kaura da kuma karamar Kauru dake Kudancin Kaduna.
Jami’in watsa labaran rundunar, ASP Mohammed Jalige, shi ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a ranar Juma’a a Kaduna.
Har wala yau Kwamishinan ya bayar da wannan umarnin ne a wani matakin ganin an dawo da doka da oda bayan da aka kara samun barkewar tashin hankali a yankin a wadannan kwanaki.
Rundunar ta yi alkawarin yin dukkanin mai yiwuwa wajen tabbatar da tsaro a yankin.