Majalisar dokokin jihar Kano tayi alkawarin yin duba na tsanaki kan daftarin kasafin kudi na shekarar 2022, da gwama Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya gabatar mata a yau, dan ganin ta amince da shi domin fara aiwatar da shi akan lokaci.
Shugaban majalisar Injiniya Hamisu Ibrahim Chidari ne ya bayyana hakan, jin kadan bayan da gwamnan Kano ya gabatar da kasafin, wanda yawan kudin da kasafin ya kunsa ya tasar ma kusan Naira miliyan 200.
Daga nan sai ya bukaci shugabannin hukumomi da ma’aikatu na gwamnati a jihar, da su kasance cikin shiri domin bayyana gaban kwamitocin zauren tare da kare kudin da aka ware musu a cikin kasafin.
Daga nan sai zauren ya dage zaman majalisar zuwa ranar Litinin ta Mako mai kamawa, bayan da shugaban Masu rinjaye na majalisar Hon. Labaran Abdul Madari mai wakiltar karamar hukumar Warawa, ya gabatar da kudirin hakan kuma ya samu goyon bayan wasu daga cikin lambobin zauren.