Rahotanni daga kasar Faransa sun bayyana cewa kungiyar kwallon kafa ta Paris Saint-Germain tana shirin daukar kyaftin din Arsenal Martin Odegaard a matsayin wanda zai maye gurbin Lionel Messi,kamar yadda Daily Post ta rahoto.
Kamar yadda wani rahoto na El Nacional ya rawaito, PSG na son siyan Odegaard bayan da ya taka rawar gani a Arsenal saboda ba a san makomar Messi da zakaran gasar Ligue 1 ta Faransa a halin yanzu ba.
KARANTA WANNAN LABARIN: Messi Ya Mayar Da Martani Yayin Da dan Wasan Barcelona Zai Bar Kungiyar
‘Yan wasan Parisiya sun ci gaba da bin diddigin tsohon dan wasan na Real Madrid kuma sun yanke shawarar siyansa akan euro miliyan 65 don kawo shi Faransa.
JARIDAR DIMOKURADIYYA ta rawaito cewa PSG za ta fafata da Bayern Munich, wadda ita ma ke zawarcin Odegaard.
Rahoton ya kara da cewa kocin Bayern Munich Thomas Tuchel shi ma babban masoyin dan wasan na Norway ne kuma ya bukaci zakarun na Bundesliga da su tashi.
A wani labarin kuma, Da Yuwuwar Yan wasan Barcelona Biyu, Su bi Messi Zuwa Sabuwar Kungiyarsa
Al-Hilal na fatan zawarcin Lionel Messi daga Paris Saint-Germain a wannan bazarar, ta hanyar kulla yarjejeniya da takwarorinsa na Barcelona Sergio Busquets da Jordi Alba. Kamar yadda Daily Post ta ruwaito.
An yi imanin cewa kungiyar ta dake buga gasar Saudi Pro League ta gabatar da kudin da ya kai fam miliyan 400 ga Messi, wanda ke shirin zama wakili na kyauta.
Ba a tsammanin kyaftin din Argentina zai kulla sabuwar yarjejeniya da PSG.
A cewar El Chiringuito, Messi ya shirya karbar tayin Al-Hilal.
An kuma yi ikirarin cewa dan wasan da ya lashe kofin duniya Busquets zai amince da kwantiragin shekaru biyu a kungiyar dake Gabas ta Tsakiya idan kwantiraginsa ya kare a Barcelona.