Ƙungiyar Miyetti Allah reshen jihar Kaduna dake Kachia ta bayar da rahoton yadda wasu mazauna yankin Zangon Kataf dake jihar Kaduna suka farmaki wasu Fulani makiyaya uku.
Sakataren kungiyar Miyetti Allah Muhammed Musa, shi ne ya bayyanawa manema labarai afkuwar lamarin, inda yace mazauna yankin sun gargaɗi makiyayan da kada su yi kiyo a yankin nasu.
Ya ƙara da cewa, a yayin komawarsu gida ne wasu matasan yankin suka farmake su kuma dukkaninsu su ukun sun samu raunuka, ɗaya daga cikinsu mai suna Suleiman yafi kowa jikkata saboda harbin bindiga da aka masa, yanzu haka dai makiyayan na karba magani a wani asibitin kuɗi dake Kachia.
“Wasu fusatattun matasa ne suka farmake su akan hanyarsu ta komawa gida, saboda sun musu kashedin kada su yi musu kiyo a yankinsu”.
“Makiyayan mazauna ƙauyen Kurmin Gwaza dake Kachia, kuma sun tafi yankin Goragam yin kiyo ne”, cewar Sakataren.
Da aka tuntunbi Kakakin hukumar ‘yan sandan jihar Kaduna ASP Mohammed Jalige, domin jin ta bakinsa yace ba zai ce komai ba har sai hukumar tasu ta kammala bincike.
Sai dai wata majiya ta bayyana mana cewa lamarin ya faru da misalin ƙarfe 2 na yammacin ranar Talatar da ta gabata ne.