Mazauna yankin Ikorodu kusa da legas ranar juma’a sun tashi da kaduwa yayin da aka ga gawarwakin uba, mata da kuma dansu a bangaren da suke zaune.
Majiyar mu ta gano cewa abun ya faru ne a lamba 12, Obafemi Erija Barokini a yankin Aga dake ikorodu da misalin karfe 6:30 na safe.
Makwabcin mamatan Mista Taiwo Salami,ya fadawa majiyar mu mamacin mai suna Charles Omomo Wanda aka fi Sani da Baba Efe,da mai dakin sa Faith omomo da yaran su uku suna ciki lokacin da abun ya faru.
Yace na bar gida da wuri kamar yadda na saba da mashin di na bayan wasu lokutta matata ta kirani ta ce an ga Gawar Baba Efe da iyalansa a bangaren su.
Yayin da na Isa gida naga taron mutane da na shiga bangaren Baba Efe sai na fahimci ya kashe kanshi matar kuma gawar ta na kasa dansu kuma yana kan kujera shima a mace.
Nayi mamaki saboda jiya da daddare naga miji da matar a zaune kamar yadda suka saba har suna wasa da juna,ban san mai ya haddasa hakan ba inji Salami.
Yace yaran suna tare da iyayen nasu a wannan lokacin .
Babbar ‘Yar Efe ta tafi wajen wasu daga cikin dangin su Wanda suke kusa ta fada musu abun da ya faru cikin firgici.
Mamacin da yake aikin Achaba amma ya daina watanni uku baya saboda matsalar da mashin din ya samu sannan yaran sun daina zuwa makaranta kuma ko jiya Dana gansu babu alamar rashin jindadi ko damuwa tare da su.inji Salami.
Wani Makwabcin Wanda baya son a fadi sunan shi yace omomo da matarshi sun samu hatsaniya kwanakin nan.inda Mijin yake cewa matar ita ta je fa shi halin da yake ciki sannan sai ta fada mishi waye asalin uban danshi.
Kamar yadda kuka gani uba da matar da yaran suna tare kuma ba abinda ya faru da sauran ‘ya’yan sai wannan namijin, inda su uku ne suka mutu.
Mai magana da yawun ‘Yan sandan jahar legas DSP Bala Elkana bai mayar da amsa ba kan tambayar da aka mishi, game da Aukuwar lamarin.