Karamin ministan ayyuka da gidaje Umar El-yakub ya ce za a kammala aikin titin Kano zuwa Gwarzo zuwa Dayi kafin karshen wannan shekara.
Kamfanin dillacin labarai na kasa NAN ya rawaito, El-Yakub ya bayyana haka ne a lokacin da yake duba aikin titin Kano-Dowakim-Tofa-Gwarzo- Dayi da Kano western bypass a jihar ta Kano.
Ya ce hanyoyin idan aka kammala za su taimaka matuka wajen bunkasa harkokin kasuwanci a yankunan baya ga samar da ayyukan yi.
“Manufarmu ba kawai mu tsaya a Abuja mu jira bayanai daga ma’aikatanmu da ‘yan kwangila ba. Daga lokaci zuwa lokaci, ma’aikatar ta kan yi tafiya da kanta a kan tituna kuma ta tantance su da kanta.
“Na duba ayyukan tituna da hannu na kuma da matakin kammalawa, zan iya cewa yaushe ne za a iya kammala ayyukan,” inji shi.
Ya ce ayyukan da aka yi wata hanya ce ta tsakanin jahohin da ke bukatar sake ginawa da sabunta su daga darajar titin mota daya zuwa titin mota biyu.
“Titin Kano zuwa Gwarzo zuwa Dayi mai tsawon kilomita 83.42 ne wanda ya hada da gadoji uku kuma babbar hanya ce a yankin arewacin Najeriya da ta hada Kano da jihohi da dama a shiyyar arewa maso yamma da arewa ta tsakiya.” Inji shi.
Ya ce idan aka kammala, za a kuma rage zirga-zirgar ababen hawa sannan kuma lokacin tafiya zai yi sauri yayin da za a samar da ayyukan yi ga jama’ar yankin.
“Haka kuma zai bunkasa harkokin zamantakewa da tattalin arziki tsakanin jihohin Kano da Katsina,” inji shi.
Ya ce ana ci gaba da gudanar da irin wannan binciken a jihar Katsina domin tabbatar da cewa mazauna yankin sun samu damar shiga ayyukansu da wuraren kasuwanci kyauta.
Dimokuradiyya ta rawaito cewa, Ministan wanda ya kuma duba aikin gina gidaje na tarayya ya nuna farin cikinsa da cewa masu amfani da layin sun mamaye gidajen.
Ya ce ayyukan gidaje na kasa a kashi na daya da na biyu kuma sun fara aiki a fadin kasar nan a shekarar 2016 a wani bangare na manufofin shugaban kasa Muhammadu Buhari.
Ya ce ana sa ran za a gudanar da ayyukan gidaje a matakai uku, yayin da aka yi nasarar aiwatar da na biyu cikin nasara,” inji shi.