Dr Ramatu Aliyu ta bayyana hakan ne a yayin da ta kai wa Mai Martaba Ohimege Igu Agabaido, Alhaji Abdulrazak Koto, ziyara a fadarsa a ranar Talata a karamar hukumar Koton Karfe a jihar Kogi.
Karamar ministar Abuja, Dr Ramatu Aliyu ta bayyana matukar aka sake zabar gwamnan Yahaya Bello na jihar Kogi a karo na biyu da mataimakinsa, Edward Onojo, to tabbas zai kawo gyara da ci gaba a bangaren tattalin arziki da zamantakewa wajen ci gaban jihar.
Ministar ta ce ta kawo ziyarar ne domin neman sanya albarkar Sarkin bisa neman zabar dan takararsu na jam’iyyar APC a zaben 16 ga watan Nuwamba a jihar.
Ta kara da cewa zaben wanda yake kai a yanzu, hakan zai taimaka wajen ci gaba da samun ayyukan gwamnatin tarayya a jihar, tare da kuma samun kyakkyawan shugabanci wanda hakan zai sanya al’ummar jihar su sharbi romon dimukradiya.