Wasu ‘yan siyasa ne suka tafi yawon kamfe a hanyar su ta dawowa sai sukayi hatsari kowa da kowa ya mutu, can saiga wani bafulatani yazo ya iske su ba mai rai sai ya yanke shawarar haka rami ya birne su baki daya, bayan ya haka ramin sai ya fara sasu daya bayan daya duka a rami daya, can sai yaga wani na motsi cikin su bai karasa ba yana cewa dan Allah ka taimake ni ka cire ni ban mutu ba, budan bakin dan Fulani sai yace “kaji ‘yan siyasa karya wa zakama karya ai kowa ya sanku haka kuke da karya” ya mutu wai yana karyan bai mutu ba hhhhhhhhhhhhhhhh