Dalibai a jihohin Imo da Oyo a ranar Juma’a sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da ci gaba da yajin aikin kungiyar malaman jami’o’i ta kasa wato ASUU.
Daliban sun toshe manyan tituna a jihohin, lamarin da ya sa aka hana zirga-zirgar ababen hawa na sa’o’i da dama.
A Imo, daliban karkashin inuwarsu – kungiyar daliban jihar Imo ta kasa (NAIS) sun sha alwashin rufe manyan titunan jihar idan ASUU da gwamnatin tarayya ba su warware sabanin da ke tsakaninsu ba nan da kwanaki bakwai masu zuwa.
Daliban na dauke da alluna dauke da rubuce-rubucen da ke nuna fushinsu, inda suka zargi gwamnatin tarayya da ASUU da yin aiki da bai dace ba ga daliban Najeriya.
Shugaban Majalisar Dattawan kungiyar ta NAIS, Alfred Jacinta, ya zargi gwamnatin tarayya da kawo musu cikas, a lokacin da makomarsu ke cikin mawuyacin hali.
A jihar Oyo, daliban jami’ar Ibadan sun tare manyan titunan da ke zuwa babban garin Ibadan daga titin Ilorin zuwa Ibadan, inda suka rika rera taken “Akawo Karshen yajin aikin ASUU yanzu”.
Majiyar Jaridar Dimokuradiyya a ranar Asabar din da ta gabata ce ta ruwaito cewa, an jibge jami’an tsaro a yankin da daliban ke zanga-zanga domin dakile tabarbarewar doka da oda.
Wani dalibi mai mataki karatu na 200level na Jami’ar Ibadan, Solomon Emiola, wanda ya jagoranci zanga-zangar, ya ce zanga-zangar ta zama dole saboda dalibai sun gaji da zama a gida.
“Shugabannin mu na cigaba da siysantar da makomarmu. Burinmu shi ne mu rufe Ibadan gaba daya har sai an biya mana bukatarmu,” in ji dalibar.
Ya kuma bayyana cewa za a ci gaba da zanga-zangar a kullum har sai gwamnati ta saurari bukatun dalibai.
Da take magana da manema labarai, Emelieze Andrew, tsohuwar shugabar kungiyar ‘yan kasuwa (TUC), ta ce an shirya zanga-zangar ne domin tada hankulan daliban da gwamnati ta take musu hakkinsu.
Andrew ya ce yajin aikin ASUU ya samo asali ne sakamakon sakaci da gazawar shugabanci