Rundunar sojojin ruwan Najeriya NNS Pathfinder ta ce ta ceto mutane 7 da aka yi garkuwa da su a mashigin ruwan Rivers da Bayelsa.
Kwamandan rundunar Kwamandan NNS Pathfinder da ke Fatakwal, Commodore Suleiman Ibrahim ne ya shaidawa manema labarai a Fatakwal ranar Talata cewa wani Victor Padi ne ya shirya sace mutanen.
Ya ce wadanda aka yi garkuwa da su suna kan hanyar su ne daga Bonny zuwa Fatakwal kafin a sace su.
“A ranar 10 ga watan Mayun 2022, mun sami wani mummunan lamari na yin garkuwa da mutane inda wasu fasinjojin da ke cikin jirgin ruwan kasuwanci daga Bonny zuwa Fatakwal, ‘yan fashin suka kama su kuma suka yi garkuwa da su zuwa wani wuri da ba a sani ba. Da bayanin ya riske mu sai muka tattara muka fara bin diddigin wadanda suka aikata wannan laifi a zahiri”.
Ibrahim ya ci gaba da cewa, “Bayan an gudanar da bincike, an gano cewa wani Victor Padi ne ya shirya wannan aika-aikar. Daga nan ne muka matsa muka kai farmaki sansaninsa amma abin takaici da muka isa sansanin ya sake tserewa da wadanda abin ya shafa. Bayan hadin gwiwa da dama da wasu abokan hulda, mun gano cewa ya koma wani wuri a jihar Bayelsa.
“Nan da nan muka fito daga jihar Ribas muka hada kai da sansanin mu da ke Bayelsa muka kutsa cikin sansanin inda ya kwashe wadanda abin ya shafa. Ya kara motsa su domin ya fahimci yanayin da ake ciki sosai.
“Lokacin da muka isa wuri na biyu mun matsa masa lamba kuma aka ba wa abokan aikin sa wa’adi kuma kamar yadda Allah ya kaimu ranar 21 ga watan Mayu, 2022, an ceto wadanda abin ya shafa ba tare da wani rauni ba,” in ji shi.
Ya ce dakarun sojin ruwan Najeriya sun kona sansanoni biyu na maharin da ya yi garkuwa da mutanen, yana mai cewa ana kokarin kama shi.
Wadanda aka ceto za a mika su ga iyalansu bayan an duba lafiyarsu domin sanin halin da suke ciki.
Ya kuma baiwa mazauna jihar Ribas da ke bi ta magudanun ruwa tabbacin kare lafiyarsu yana mai cewa rundunar sojojin ruwan Najeriya za ta ci gaba da aikin tare da jami’an ‘yan sanda a magudanar ruwa domin baiwa mazauna jihar damar gudanar da sana’o’insu na yau da kullun
Daya daga cikin wadanda aka kubutar, Jude Isabo ya bayyana cewa, ‘yan ta’addan sun tsare su ne a cikin mummunan yanayi inda suka karbi sama da Naira Milliyan daya daga wajensu.