Tun kafin a rantsar da wannan gwamnati a shekarar Dubu biyu da sha biyar (2015) jami’an gwamnati kama daga shugaban k’asa zuwa Jami’an (EFCC) kan shelanta maidowa gamida kwato kudade daga wurin barayin gwamnati, Wanda yawansu ya wuce miliyoyi ko biliyoyi yakai tiriliyoyi.
Sannan shugaban k’asar nijeriya muhammadu Buhari yana ambata cewa; Yasan halin kunci da kuma fatara da mutanen najeriya suke ciki, Alhalin ga wadannan kudade da ake ikirarin an kwato.
Babu yadda za’ayi shugaba Buhari ya fita daga zargin mutanen najeriya akan cewa akwai sakacinsa akan fadawar wannan kasa da kuma mutanenta cikin k’angi, tunda yasan matsalar nijeriya kuma akwai maganin a aje.
Idan da anayi domin talakkawane to babu shakkah wannan tiriliyoyi kan iya canja rayuwar mutanen nijeriya cikin kankanin lokaci.
Idan wannan kudi Na aje to wallahi anci amanar talakka a wannan k’asa tunda hakin sune, Idan bazasu amfanaba to kwatowar bata da fa’ida.
Idan kuma kudinnan basanan dolene muce ja ya fado ja ya dauka, ma’ana barawo ya Sato barawo ya sace.