By Abbas Yakubu Yaura
Akalla mutane 17 ne suka mutu yayin da 59 suka jikkata a ranar Alhamis sakamakon fashewar wani abu da ya lalata wani yankin gari a yammacin Ghana bayan wata babbar mota dauke da bama-bamai ta yi karo da babur, in ji gwamnati.
Ministan yada labaran kasar Kojo Oppong Nkrumah ya bayyana cewa, an tabbatar da mutuwar mutane 17, sannan an ceto mutane 59 da suka jikkata.
Wata babbar mota dauke da bama-bamai ta yi karo da wani babur a yammacin kasar Ghana jiya Alhamis, lamarin da ya yi sanadin fashewar wani abu mai girma da kuma asarar rayuka, in ji shugaban na Ghana.
Hatsarin ya afku ne da tsakar rana a yankin Apiate, kusa da birnin Bogoso mai tazarar kilomita 300 (mil 180) a yammacin babban birnin Accra mai arzikin ma’adinai.
Nana Akufo-Addo ya ce fashewar ta haifar da “asarar rayuka da lalata dukiyoyi”, Nana Akufo-Addo ya kara da cewa a wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter:
‘Yan sandan yankin sun fitar da wata sanarwa da ke cewa “bincike na farko ya tabbatar da cewa wata motar hakar ma’adinai dauke da bama-bamai ta yi karo da wani babur wanda ya yi sanadiyar fashewar”.
Sanarwar ta ce, “An ceto akasarin wadanda abin ya shafa” kuma an kai su asibitoci daban-daban.
Dr Joseph Darko, wanda ke aiki a asibitin Apiate, ya shaidawa kamfanin dilancin labaren AFP cewa an kai biyar daga cikin wadanda suka jikkata zuwa Asibiti, “ciki har da wani yaro dan shekara biyar da ke cikin wani yanayi na barazana ga rayuwa”.
‘Yan sanda sun bukaci kauyukan da ke kewaye da su bude makarantunsu da coci-coci don daukar duk wani karin asarar da aka samu.
Rundunar ‘yan sandan ta kara da cewa, an baza jami’an tsaro zuwa wurin da lamarin ya afku, kuma an bukaci mutanen da ke kusa da bom din da su kaura zuwa kauyukan da ke kusa.
Ghana dai ta sha fama da fashewar iskar gas a ‘yan shekarun nan sakamakon zukar mai.
A shekara ta 2017, akalla mutane uku ne suka mutu, wasu da dama kuma suka jikkata, bayan da wata motar dakon mai dauke da iskar gas ta kama wuta a birnin Accra, lamarin da ya janyo fashe-fashe a gidajen mai guda biyu tare da kashe mutane uku.
Babban birnin Ghana ya kasance wurin da aka samu irin wannan gobara da fashewa a cikin watan Yunin shekarar 2015 lokacin da mutane fiye da 150 suka mutu yayin da suke neman mafaka daga ruwan sama na yanayi da kuma ambaliyar ruwa a gidan mai. Ana kyautata zaton gobarar ta tashi ne ta hanyar man fetur a kan ruwan.
Lamarin dai ya janyo cece-ku-ce a tsakanin wasu ‘yan kasar ta Ghana a shafukan sada zumunta game da tsaron gidajen mai, wadanda yawancinsu suna kusa da makarantu, gidajen asibitoci da wuraren kasuwanci.