Jami’ar Bayero Kano (BUK), ta ce ta kammala shirye-shiryen yaye dalibai 16,581 a zangon karatu na 2018/2019 da 2019/2020.
Mataimakin Shugaban Jami’ar Farfesa Sagir Abbas ne ya bayyana haka a wani taron manema labarai na share fage da aka yi ranar Alhamis a Kano.
Jaridar DIMOKURADIYYA ta tattaro cewa Abbas ya ce za a kuma bayar da shaida manyan digiri da kyautuka ga daliban da suka kammala karatun digiri na biyu a fannin kasuwanci ta Dangote a dakin taron ta na 36 da 37 da aka shirya gudanarwa a ranar 7 ga watan Janairu.
KARANTA HAKANAN Jami’ar Bayero Ta Musanta Yin Karin Kudin Makaranta Ga Dalibai
Ya yi bayanin cewa jimillar dalibai 7,362 da za su kammala karatun digiri na farko a shekarar 2018/2019 da kuma 9,219 na 2019/2020 daga tsangayu 16 ne za su yaye.
Ya kara da cewa dalibai 8,777 da suka kammala karatun digiri na biyu, wadanda suka hada da 3,671 na shekarar 2018/2019 da kuma 5,106 na shekarar 2019/2020 daga makarantar koyon karatun digiri na biyu da kuma makarantar kasuwanci ta Dangote.
Ya bayyana cewa 285 daga cikin wadanda suka kammala karatun digiri na farko sun fita da mataki na farko, 359 daga cikin wadanda suka kammala digirin za su sami PHD; 5,936 za su sami Digiri na biyu, yayin da za a ba da Difloma a kan mabukata 2,484.
Jaridar SOLACEBACE ta rawaito cewa Abbas ya ci gaba da cewa duk wadanda suka kammala karatun da za su halarci taron za su karbi satifiket dinsu a rana guda.
Ya ce shugabanni da majalisar gudanarwar cibiyar sun yanke shawarar ba za su ba da wani digiri na girmamawa ba yayin taron.
Ya ce cibiyar ta ci gaba, har ma ta samu ci gaba a fannin ilimi a cikin shekara guda da ta wuce.
Ya bayyana cewa duk shirye-shiryen da jami’ar ta gabatar don karramawa daga hukumomi na yau da kullun da kwararrun sun samu karbuwa. (NAN)
A Wani Labarin Kuma Babu Wani Shiri Daga Jami’an NSCDC Don Kauracewa Zabe — Hukumar
Hukumar kula da kadarorin gwamnati da tsaron al’umma NSCDC, ta kafa wani kwamiti da zai gaggauta bin diddigin biyan alawus-alawus na ma’aikatan da suka gudanar da zaben Osun da Ekiti a shekarar 2022.
Mista Olusola Odumosu, daraktan hulda da jama’a na NSCDC, ya bayyana haka a ranar Alhamis a Abuja cewa, gwamnatin tarayya ta saki kudaden domin a biyan kudin.