Wani bincike ya nuna cewar akalla mutane 415 aka kashe a Nijeriya a watan Yulin da ya gabata sakamakon hare-hare da kuma tashin hankalin da ake ci gaba da samu a cikin kasar kamar yadda shafin RFI Hausa ya tabbatar.
Wata kungiya da ta kira kan ta ‘Nigeria Mourn’ ta ce an fi samun kashe-kashen dake da nasaba da hare-haren ‘yan bindiga da rikicin Boko Haram da kuma barayin shanu ne a Jihohin Kaduna da Borno da Katsina.
Alkaluman kungiyar sun ce daga cikin Jihohi 21 da aka kashe mutane 415, Jihar Kaduna ke sahun gaba da mutane 139, sai Barno mai 113, Katsina na da 80, Kogi 17, Nasarawa 13, Taraba 10, Binuwe 9 sai kuma Ebonyi mai 8.
Sauran sun hada da Zamfara mai mutane 7, Filato 5, Edo da Akwa Ibom da Legas na da bibiyu, sai kuma Jihohin Oyo da Imo da Ribas da Kuros Ribas da Ogun da Bayelsa da Delta da kuma Kebbi dake da daya-daya.