Mutane 5 ne suka mutu yayin da wasu biyu suka samu raunuka a wani hatsarin mota kirar Golf Volkswagen da kuma babur na (Adai Daita Sahu) a kan hanyar Kwanar Dumawa zuwa Kunya a karamar hukumar Minjibir ta jihar Kano.
Da yake tabbatar da faruwar lamarin, kwamandan hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC) a sashin Zubairu Mato, ya ce hatsarin ya afku ne sakamakon gudun wuce kima.
Ya ce mutane biyar (maza hudu da mace daya) sun rasa rayukansu yayin da biyun da suka samu raunuka maza ne.
A cewarsa, bayan samun rahoton afkuwar hatsarin, tawagar hukumar a Dake aiki a ofishin Minjibir ta isa wurin da lamarin ya faru, inda suka kai wadanda lamarin ya rutsa da su zuwa manyan asibitocin Minjibir da Danbatta inda likita ya tabbatar da mutuwar mutane biyar daga Cikin su.
KARANTA WANNAN LABARIN: Bututun Iskar Gas na Kwarara a Legas
Ya kara da cewa mutanen biyu da suka jikkata a halin yanzu suna karbar magani a asibiti.
“Mun samu waya da misalin karfe 1:05 na rana ranar Talata. Da samun labarin, sai muka yi gaggawar aika jami’an mu da motar mu zuwa wurin da lamarin ya faru, domin ceto wadanda lamarin ya shafa da karfe 1:10 na rana”
“Bayan isar mu da su asibiti, likitan da ke bakin aiki ya tabbatar da mutuwar mutane biyar a cikin wadanda abin ya shafa,” in ji Mato.
Ya kara da cewa motocin biyu da abin ya shafa sune Volkswagen (Golf) mai lamba DUT449 CZ dakeke Napep kirar Bajaj Tricycle mai lamba GWL 51 WG.
Idan za’a iya tunawa ko a makon da ya gabata ma dai an samu irin wannan hatsari a yankin Kano Ta Arewa, inda Dalibai biyar na kwalejin ilimi ta Sa’adatu Rimi suka rasa rayukansu yayin da wasu da dama suka jikkata