Ministar agaji da kyautata rayuwar al’umma Sadiya Umar Farouk ta sanar da rufe rijistar neman aikin N-Power yayin da sama da mutum miliyan biyar ne suka nemi aikin.
Wata sanarwa da Ministar Agaji da kyautata rayuwa Sadiya Umar Farouk ta fitar na cewa mutum 5,042,001 ne ke neman a ɗauke su aikin wanda aka rufe wa’adin yin rijistar a ranar 9 ga watan Agusta 2020.
“Ma’aikatar ta tabbatar da cewa waɗanda suka cancanta ne kawai za a fitar da sunayensu kuma za a tuntube su, sannan a wallafa sunayensu”, kamar yadda Ministar ta sanar.
Sadiya Farouk ta ƙara da cewa, za a bai wa mata da masu naƙasa muhimmanci a guraben aikin.
A cewarta shirin N-Power an ƙirƙiro shi ne don samar wa matasan Najeriya ayyukan yi, wanda hakan zai taimaka wa ƙasar nan daga farfadowa daga halin ƙuncin da jama’a suka samu kansu a wannan lokaci na annobar Korona.