By Abbas Yakubu Yaura
Akalla mutane uku ne aka tabbatar da mutuwarsu, yayin da wasu biyu suka samu munanan raunuka sakamakon ruftawar ginin wani shago a wata kasuwar al’umma dake jihar Ebonyi.
An gano cewa rufin daya daga cikin rumfunan budaddiyar kasuwar ya kone a yammacin ranar Juma’a.
An kuma kara da cewa lamarin ya faru ne a dandalin Kasuwar Ekeaja, Uburu, cikin karamar hukumar Ohaozara ta jihar, mahaifar Gwamna David Umahi.
Gwamna David Umahi ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar.
Umahi, a cikin sanarwar, wacce mai taimaka masa na musamman kan harkokin yada labarai, Nwaze Francis, ya bayyana, ya nuna rashin jin dadinsa kan wannan mummunan lamari daya afku.
Sanarwar ta kara da cewa, “Gwamnan jihar Ebonyi, David Umahi, ya kadu da jin labarin ruftawar wani sashe na rufin daya daga cikin shagunan da ke kasuwar Ekeaja, Uburu, wanda ya yi sanadin samun asarar rayuka kusan uku, yayin da wasu biyu ke kwance a asibiti.”
Umahi, wanda ya bayyana lamarin a matsayin bala’i, ya kuma jajanta wa iyalan mutane ukun da suka rasa rayukansu.
Sanarwar ta kara da cewa, “Mun samu labarin wani mummunan al’amari na ruftawar wani bangare na daya daga cikin shagunan kasuwar Ekeaja da kuma mutuwar mutane uku a lamarin cikin juyayi.
“A matsayinmu na ’yan adam, ba za mu iya tambayar Allah ba, amma muna addu’a ga Allah Madaukakin Sarki da Ya ba wadanda abin ya shafa hutu ya kuma yi wa iyalansu ta’aziyya.
“Duk da haka, muna addu’ar Allah Madaukakin Sarki ya ba wadanda suke kwance asibiti sauki cikin gaggawar tare da dawowar su cikin
iyalan su.”
Gwamnan ya umurci ‘yan sanda da sauran hukumomin da abin ya shafa da su gaggauta gudanar da cikakken bincike domin gano musabbabin faruwar lamarin nan take.