Mutanen Garin Lafiya na Tafiyar kilomita 200 don Zuwa Babban Asibiti
Umar Tanko Al-makura Dan majalisa mai wakiltar Nasarawa ta Yamma yace Mutanen dake zaune a garin lafiya suna cikin wani hali na rashin babban asibitin koyarwa a garin.
KARANTA:- Na kama yar aikina turmi da tabarya da dan cikina mai shekara 10
Yace hakan bai dace ba ace Mutanen Nasarawa har sai sunyi tafiyar kilomita 200 domin cimma babban asibiti.
Yace dayawa daga cikin Mutane suna rasa rayukansu na kokarin zuwa irin wannan manyan Asibitocin.
Yace idan ka duba inda Lafiya take a Nasarawa zakaga Mutane dake garin sai sunyi tafiyar kilomita 200 kamin su cimma babban asibiti Kuma wannan bai dace ba a wannan karnin.
Dan majalisan yace ana da bukatar asibiti koyarwa a wannan duba da irin rasa rayuka da Mutanen yankin keyi.
Sai dai Dr. Osage Ehanire ministan Lafiya yayi bayani nan da dan lokaci kadan za’a fara aikin asibitin garin Keffi dake Nasarwa zuwa Asibitin Koyarwa.
Yace gwamnatin tarayya na cigaba da duba Asibitocin gwamnatin tarayya zuwa Asibitin Koyarwa a fadin kasar.
Bayan ji daga bakin Mutane, shugaban Yan Majalisun na fannin Lafiya Ibrahim Yahaya O. Yace yawan Mutane zai bada damar Mika kudurin zuwa wajan Yan Majalisun.
Comments 1