Mutane 2 ne suka mutu sakamakon fashewar wata tankar Mai a Enagi, hedikwatar karamar hukumar Edati a jihar Neja.
Shaidun gani da ido sun shaida wa wakilin Majiyarmu cewa, lamarin ya faru ne da misalin karfe 11 na safiyar yau Lahadi.
Wata shaidan gani da Ido mai suna Hassan, wanda shi ma ya rasa shagon sa da ke gefen titi, ya shaida wa wakilinmu majiyar Jaridar Dimokuradiyya ta wayar tarho cewa, motar dakon mai dauke da man Fetur ta yi karo da wata babbar mota kirar kamfanin Dangote.
“Kankar ta fito ne daga Mokwa a yayin da motar Dangote da ta taho daga Bida, yayin da su kayi taho mugama da juna Wanda hakan yasa tankar ta fashe.”
KARANTA WANNAN LABARIN: Malamai 8 sun hallaka yayin Nutso domin Dauko Sanda Mai Tsarki
“Shagunan da dama, babura a gefen hanya da gine-gine sun shafi,” in ji shi.
Wani shaida kuwa mai suna Mohammed Kitabu Enagi ya ce: “Ya zuwa yanzu, gawarwaki biyu ne kawai aka gano.sanadiyar lamarin” a cewar shi.
“Amma akwai motoci da dama da suka kone kurmus, Ba a cire su ba, Kuma ba’a tabbatar ba ko an samu karin asarar rayuka.”
Kwamandan hukumar kiyaye haddura ta kasa reshen jihar Neja Musa A. Mohammed ya tabbatarwa da wakilin Jaridar Daily Trust faruwar lamarin.
Comments 1