Cibiyar dake dakile cututtuka masu yaduwa ta Nijeriya, NCDC a daren ranar Laraba ta tabbatar da cewa an samu karin mutum 91dake da korona a Nijeriya.
NCDC ta tabbatar da hakan ne a sakon da ta wallafa a shafinta na Twitter. Cibiyar ta ce; an samu karin mutum 74 a Legas da kuma 5 a Katsina.
Ya zuwa yanzu mutum 873 ke da korona a Nijeriya. A yayin da mutum 28 suka mutu daga cutar. Inda kuma 197 suka warke.
Ga jerin mutum 91 din da suka kamu aka tabbatar a jiya.
74 a Legas
5 a Katsina
4 a Ogun
2 a Delta
2 a Edo
1 a Kwara
1 a Oyo
1 a FCT
1 a Adamawa