Mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbanjo ya bayyana cewa gwamnati za ta tallafa wa mutum 9,000 da kudade da kayan aiki domin fara sana’ar kiwon kifi a jihar Kebbi.
Osinbajo ya fadi hakan ne a taron kaddamar da shirin tallafa wa mutane domin fara sana’o’in hannu na shirin ‘Tradermoni’ da aka yi Birnin Kebbi ranar Alhamis.
Ya ce burin gwamnati shi ne kafa cibiyoyi na sana’o’in hannu a kalla guda daya a kowani jiha a kasar nan.
Tun a 2017 ne gwamnati ta kaddamar da wannan shiri, zuwa yanzu kuwa an tallafa wa mutum 400,000 a fadin kasarnan.
Majiyarmu ta labarto cewa; jihar Kebbi ce jiha ta 24 da zai ci moriyar wannan shiri na gwamnatin tarayya wanda mutum 9000 za su samu tallafin.
A karshe Osinbajo ya yi kira ga hukumomi da masana’antu da su rika tallafa wa da bai wa shirin gwamnati goyon baya domin samun nasara a kai.