Mutumen da yayi Safarar Matar shi don Karuwanci, ya saida Ɗan sa N600,000
Jami’an Rundunar Ƴan Sandan Jahar Ogun sun kama mai shekaru 36 mai suna Kinsley Essien da zargin Safarar matar shi zuwa Ƙasar Mali domin tayi Karuwanci tare da saida Ɗan ta mai shekaru 2 kan Naira N600,000.
Mai Magana da Yawun Rundunar Ƴan Sandan Jahar DSP Abimbola Oyeyemi a cikin Sanarwar daya fitar a ranar Alhamis, yace an kama wanda ake zargin biyo bayan samun wani rahoto a Caji-ofis na Ƴan Sanda, wanda Matar sa ta kawo Bright Essien.
KARANTA WANNAN LABARIN: Kungiyar kwallon Kafa ta Leicester Tayi Kunnen Doki Da Chelsea
Mai Magana da Yawun Rundunar Ƴan Sandan Jahar yace “Bright ta kawo rahoto cewa wani lokaci a watan Oktoba na Shekarar 2021, Mijinta Kinsley Essien, ya sanar da ita cewa ya samu aiki, kuma ya taimaki mutane da dama zuwa Ƙasar domin neman kuɗi.
“Ta bayyana cewar a matsayin ta Mijinta, ba tayi tunanin komai ba, har saida taje Ƙasar Mali, inda ta gano cewa an saida ta ga wata Magajiyar Karuwai akan Naira miliyan 1,400,000..
” A lokacin da take a Mali an tilasta mata yin Karuwanci, amma daga baya ta gano ofishin Jakadancin Najeriya a Bamako, inda aka taimaka mata ta dawo Najeriya.
“Lokacin da ta dawo ta gano Ɗan ta mai Shekaru 2 dake ƙarƙashin kulawar mijinta baya nan.
“Bayan samun wannan rahoto, DPO na Agbara SP Abiodun Salau ya umarci jami’ai dasu bi bayan shi, inda suka Kamo shi, kuma bayan bincikar sa ya tabbatar da aikata laifin da ake zargin, yana mai cewa ya saida Ɗan kan Naira 600,000.
Kakakin Ƴan Sandan yace Kwamishinan Ƴan Sandan Jahar Lanre Bankole ya bada umarnin Kamo wanda ya sayi Ɗan.
Comments 1