Daga wakilin Dimukaradiyya Mukhtar Yakubu Kano.
Fitacciyar jaruma a Masana’antar fina-finai ta Kannywood Masauda Ibrahim wacce aka fina da Yar’agadaz ,wacce kuma ta yi suna a cikin shirin Dadin Kowa wato Zuby, ta bayyana irin wahalar da ta sha a harkar fim kafin ta samu ta zama fitacciyar jaruma.
Masa’uda’ Yar’agadaz ta bayyana hakan ne a lokacin tattaunawarta da wakilin Jaridar Dimokuradiyya, inda ta fara da cewar :
“To gaskiya na sha wahala, kuma na hadu da Kalubale da dama a cikin harkar fim musamman ma dai sai ka ga wani ya nuna yana son ka a fili, sai ka tafi kuma ya zage ka, to irin wannan na fuskance su da dama, sai dai ina yi musu fatan alheri, saboda yanzu komai ya wuce a waje na, domin idan na ce zan tsaya na lissafa to abubuwan suna da yawa. ”
Dangane da maganar aure kuwa da muka tambaye ta cewa ta yi:
KARANTA WANNAN LABARIN: An tsaurara Tsaro a Abia yayin da Kotu ke sauraron karar Namdi Kanu
“Ni dai a gare ni zabin Allah na ke nema, duk wanda Allah ya zaba miun shi zan aura, don haka duk masu yi mana kallon muna da buri, to mu ba haka mu ke ba, domin arziki na Allah ne, don haka ba sai lallai mai kudi zan aura ba, miji nagari kawai na ke fatan samu. ” a cewar ta.
A wani labarin na daban.
Yunkurin juyin mulkin da akaso ayi a Sudan “ya ci tura” da sanyin safiyar Talata, in ji kafofin yada labarai na kasar, yayin da kasar ke fama da sauyin yanayi mai rauni tun bayan kawar da tsohon shugaban kasar Omar Al-Bashir a shekarar 2019.
Manyan majiyoyin soji da na gwamnati sun shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa yunkurin ya shafi gungun jami’an da aka “dakatar da su nan take” bayan da suka “kasa” kwace ginin kafafen yada labarai na jihar.Gidan talabijin na kasar ya ce, “An yi yunkurin juyin mulkin da bai yi nasara ba, ya kamata mutane su tunkare shi,” ba tare da yin karin bayani ba.
Wani babban jigo a hukumar mulki ta Sudan, Taher Abuhaja, ya ce “an dakile yunkurin kwace mulki.” Wani babban memba na hukumar mulki, Mohamed al-Fekki ya ce, “Komai yana karkashin ikonsa kuma juyin juya halin ya yi nasara.”
Da alama zirga zirgar ababen hawa na gudana cikin kwanciyar hankali a tsakiyar Khartoum, kamar yadda wakilan AFP suka ruwaito, gami da kewayen hedikwatar sojoji, inda masu zanga zangar suka yi zaman dirshan wanda a ƙarshe ya kai ga kawar da Bashir a wani juyin mulkin.Sai dai jami’an tsaro sun rufe babbar gadar dake haye kogin Nilu dake hada Khartoum da tagwayen birnin Omdurman.
A halin yanzu Sudan tana karkashin gwamnatin rikon kwarya wacce ta kunshi wakilan farar hula da na sojoji wadanda aka girka bayan hambarar da gwamnatin Bashir a watan Afrilun 2019 kuma an dora mata alhakin kula da dawowar cikakken mulkin farar hula.
Gwamnatin, karkashin Firayim Minista Abdalla Hamdok, ta sha alwashin gyara tattalin arzikin kasar da ke fama da tabarbarewar zaman lafiya tare da kungiyoyin ‘yan tawaye da suka yaki gwamnatin Bashir.
A ranar Litinin, masu zanga zangar sun toshe manyan hanyoyi da babbar cibiyar kasuwanci ta kasar, Port Sudan, don nuna adawa da yarjejeniyar zaman lafiya da aka kulla da kungiyoyin ‘yan tawaye a bara.