• About Us
  • Blog
  • Gwamnatin Jihar Kano ta ce ana gabda fara ginin masana’antun Iskar Gas a Jihar
  • Home
Monday, March 20, 2023
  • Login
Dimokuradiyya
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Rahotanni
  • Wasanni
  • Rikicin Duniya
  • Nishadi
  • More
    • Kasashen Ketare
    • Kiwon Lafiya
    • Ilimi
    • Kasuwanci
    • Noma Da Kiwo
    • Labarun Mako
    • Talla
    • Masarautu
    • Babu Maraya
    • Addini
      • Wa’azin Kirista
    • Girke-Girke
    • Waiwaye
    • Marubutanmu
    • Wasiku
    • Ni’ima Dai Mata
    • Tsaro
    • Bidiyo
    • Audio
No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Rahotanni
  • Wasanni
  • Rikicin Duniya
  • Nishadi
  • More
    • Kasashen Ketare
    • Kiwon Lafiya
    • Ilimi
    • Kasuwanci
    • Noma Da Kiwo
    • Labarun Mako
    • Talla
    • Masarautu
    • Babu Maraya
    • Addini
      • Wa’azin Kirista
    • Girke-Girke
    • Waiwaye
    • Marubutanmu
    • Wasiku
    • Ni’ima Dai Mata
    • Tsaro
    • Bidiyo
    • Audio
No Result
View All Result
Dimokuradiyya
No Result
View All Result
Home Labarai

NAFDAC Ta Karyata CP Wakili ‘Singham’ A Kan Batun Kama Kwaya A Kano

Mustapha Haruna Dabai by Mustapha Haruna Dabai
May 23, 2019
in Labarai
Reading Time: 4 mins read
0 0
0
1
SHARES
5
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Babban Jami’i mai kula da Kano na Hukumar lura da abinci da magunguna ta kasa (NAFDAC), Pham. Shaba Muhammad, ya karyata wani zargi na kama tarin kwayar Tiramadol a Kano, ba kamar yadda rundunar ’yan sandan jihar ta furta ba. Babban Jami’in, ya yi wannan furuci ne a daidai lokacin da ya ke ganawa da manema labarai a jihar ta Kano. Ya ce abin da aka kama ba Tiramadol ba ne, magani ne mai kama da Paracetamol, kuma ba ya daga cikin masu illa ko bugarwa, sabanin yadda Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Kano, CP Muhammad Wakili, wanda a ka fi sani da Singham, ya yi ikirari. “Maganin da Kwamishinan ‘Yan Sandan na Kano ya kama Diclofenac Sodium BP ne, wanda ba shi da alaka da Tiramadol , amma duk da haka da maganin ya zo gabanmu a matsyinmu na masu wannan aiki na kama gurbataccen abinci ko maganin da ba shida inganci da doka ta hana a shigo da shi ko a yi amfani da shi, yanzu haka mun aika da wannan magani zuwa dakin bincikenmu don tabbatar da ingancinsa. Amma dai kafin wannan lokaci, wannan magani da Kwamishinan ‘Yan Sanda ya yi ikirarin kamawa, ba Tiramadol ba ne, magani ne da Likitoci ke rubuta wa marasa lafiya a asibiti ga masu bukatar irin sa,” in ji shi. Shaba ya ce, tsakaninsu da Rundunar Hukumar ‘Yan Sanda da kuma Hukumar yaki da sha tare da fataucin miyagun kwayoyi (NDLEA) da kuma NAFDAC, suna aiki ne kafada da kafada kuma akwai kyakkyawar fahimta a tsakaninsu, domin kuwa kowa na da bukatar kowa don samun nasarar aikin kowannensu. Sai dai kuma, a wannan karon Kwamishinan na ‘Yan Sandan Jihar ta Kano, ya yi gaban kansa wajen ikirarin cewa ya kama Tiramadol, alhalin ba haka ba ne, don haka ya shawarci Kwamishinan Muhammad Wakili, da ya rika tuntubar Hukumar ta NAFDAC, da sauran masu ruwa da tsaki a duk lokacin da irin wannan al’amari na magunguna ya taso, domin NAFDAC ce da makamantansu ke da ruwa da tsaki wajen tabbatar da sahihancin magani ko akasin haka, amma ba Hukumar ta ‘Yan Sanda ba. Akarshe, Shaba ya yi kira tare da jan hankali wajen tabbatar da samun rijistar Hukumar NAFDAC, ga masu magunguna da abinda ya shafi abinci, yin rijista abu ne mai sauki ba mai wahala ba, domin kuwa bayanai ne ake tattarawa a kan wanda ya nemi yin rijistar da kuma yin gwaje-gwajen lafiya ta yadda mai sarrafa abinci zai kasance ba shi da wata cuta mai yaduwa da za ta iya cutar da abubuwan da yake sarrafawa domin amfanin al’umma. A takaice dai, yin rijista da NAFDAC abu ne mai saukin gaske da zarar mutum ya cika ka’idar yin ta. Haka zalika, rahotanni sun bayyana cewa, a bangare guda shi ma Shugaban Hukumar yaki da sha tare da fataucin miyagun kwayoyi na Kanon, Dakta Abdul Ibrahim, ya koka game da yadda Kwamishinan ‘Yan Sandan ya yi wannan ikirari na kama magani a matsayin Tiramadol duk da kasancewar sa na wanda ba masanin magunguna ba. Wannan dalili ne ya sa ya shawarci Kwamishinan ‘Yan Sandan Kanon da ma sauran al’umma baki daya kan cewa kowa ya tsaya a iya iliminsa da aikinsa wanda hakan ne kadai zai kawo zaman lafiya da hadin kai da kuma ci gaban kasa da al’ummarta.Babban Jami’i mai kula da Kano na Hukumar lura da abinci da magunguna ta kasa (NAFDAC), Pham. Shaba Muhammad, ya karyata wani zargi na kama tarin kwayar Tiramadol a Kano, ba kamar yadda rundunar ’yan sandan jihar ta furta ba. Babban Jami’in, ya yi wannan furuci ne a daidai lokacin da ya ke ganawa da manema labarai a jihar ta Kano. Ya ce abin da aka kama ba Tiramadol ba ne, magani ne mai kama da Paracetamol, kuma ba ya daga cikin masu illa ko bugarwa, sabanin yadda Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Kano, CP Muhammad Wakili, wanda a ka fi sani da Singham, ya yi ikirari. “Maganin da Kwamishinan ‘Yan Sandan na Kano ya kama Diclofenac Sodium BP ne, wanda ba shi da alaka da Tiramadol , amma duk da haka da maganin ya zo gabanmu a matsyinmu na masu wannan aiki na kama gurbataccen abinci ko maganin da ba shida inganci da doka ta hana a shigo da shi ko a yi amfani da shi, yanzu haka mun aika da wannan magani zuwa dakin bincikenmu don tabbatar da ingancinsa. Amma dai kafin wannan lokaci, wannan magani da Kwamishinan ‘Yan Sanda ya yi ikirarin kamawa, ba Tiramadol ba ne, magani ne da Likitoci ke rubuta wa marasa lafiya a asibiti ga masu bukatar irin sa,” in ji shi. Shaba ya ce, tsakaninsu da Rundunar Hukumar ‘Yan Sanda da kuma Hukumar yaki da sha tare da fataucin miyagun kwayoyi (NDLEA) da kuma NAFDAC, suna aiki ne kafada da kafada kuma akwai kyakkyawar fahimta a tsakaninsu, domin kuwa kowa na da bukatar kowa don samun nasarar aikin kowannensu. Sai dai kuma, a wannan karon Kwamishinan na ‘Yan Sandan Jihar ta Kano, ya yi gaban kansa wajen ikirarin cewa ya kama Tiramadol, alhalin ba haka ba ne, don haka ya shawarci Kwamishinan Muhammad Wakili, da ya rika tuntubar Hukumar ta NAFDAC, da sauran masu ruwa da tsaki a duk lokacin da irin wannan al’amari na magunguna ya taso, domin NAFDAC ce da makamantansu ke da ruwa da tsaki wajen tabbatar da sahihancin magani ko akasin haka, amma ba Hukumar ta ‘Yan Sanda ba. Akarshe, Shaba ya yi kira tare da jan hankali wajen tabbatar da samun rijistar Hukumar NAFDAC, ga masu magunguna da abinda ya shafi abinci, yin rijista abu ne mai sauki ba mai wahala ba, domin kuwa bayanai ne ake tattarawa a kan wanda ya nemi yin rijistar da kuma yin gwaje-gwajen lafiya ta yadda mai sarrafa abinci zai kasance ba shi da wata cuta mai yaduwa da za ta iya cutar da abubuwan da yake sarrafawa domin amfanin al’umma. A takaice dai, yin rijista da NAFDAC abu ne mai saukin gaske da zarar mutum ya cika ka’idar yin ta. Haka zalika, rahotanni sun bayyana cewa, a bangare guda shi ma Shugaban Hukumar yaki da sha tare da fataucin miyagun kwayoyi na Kanon, Dakta Abdul Ibrahim, ya koka game da yadda Kwamishinan ‘Yan Sandan ya yi wannan ikirari na kama magani a matsayin Tiramadol duk da kasancewar sa na wanda ba masanin magunguna ba. Wannan dalili ne ya sa ya shawarci Kwamishinan ‘Yan Sandan Kanon da ma sauran al’umma baki daya kan cewa kowa ya tsaya a iya iliminsa da aikinsa wanda hakan ne kadai zai kawo zaman lafiya da hadin kai da kuma ci gaban kasa da al’ummarta.

Previous Post

An Fara Kidaya Kuri’un Zaben Da Aka Kada A Kasar India

Next Post

“Mu muka kashe ’yan canjin da muka yi garkuwa da su”

Next Post

“Mu muka kashe ’yan canjin da muka yi garkuwa da su”

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result
Arabic Arabic English English French French Hausa Hausa
  • Ya ce mun shi Dillalin Motoci ne, bayan mun yi aure na gane Makanike ne

    Ya ce mun shi Dillalin Motoci ne, bayan mun yi aure na gane Makanike ne

    2455 shares
    Share 982 Tweet 614
  • Da Ɗumi-Ɗuminsa: Ƙazamin Rikici Ya Kaure Tsakanin Shugaban Ƙungiyar CAN Da Isa Ashiru Kudan

    1995 shares
    Share 798 Tweet 499
  • Sai na yi lalata da kai na kwanaki 4 babu ƙaƙƙautawa sannan zan taimaka maka, Wata mata ga saurayi

    1693 shares
    Share 677 Tweet 423
  • Ga Irinta Nan: Budurwa Ta Koka Bayan Saurayinta Ya Ƙi Amsar Cikin Da Ya Ɗirka Mata

    1365 shares
    Share 546 Tweet 341
  • CBN Ya Sake Fitar Da Sabbin Bayani Kan Dawo Da Tsofaffin Takardun Kudin Naira

    1592 shares
    Share 637 Tweet 398
Gwamna Umahi Ya Kori Wasu Mataimakansa Sa’o’i 48 Bayan Kammala Zabe

Gwamna Umahi Ya Kori Wasu Mataimakansa Sa’o’i 48 Bayan Kammala Zabe

March 20, 2023
INEC Ta Bayyana Wanda Ya Lashe Zaben Gwamna A Jihar Filato

INEC Ta Bayyana Wanda Ya Lashe Zaben Gwamna A Jihar Filato

March 20, 2023
PDP Ta Lashe Kujeru 28 Na Majalisar Dokoki, Yayin Da APC Ta Tsira Da Hudu

PDP Ta Lashe Kujeru 28 Na Majalisar Dokoki, Yayin Da APC Ta Tsira Da Hudu

March 20, 2023
Bayan Faduwa A Zaben Sake Darewa Kujerar Sanata Nnamani Ya Bar PDP

Bayan Faduwa A Zaben Sake Darewa Kujerar Sanata Nnamani Ya Bar PDP

March 20, 2023
Mohammed Ya Sake Lashe Zaben Gwamna Karo Na Biyu A jihar Bauchi

Mohammed Ya Sake Lashe Zaben Gwamna Karo Na Biyu A jihar Bauchi

March 20, 2023
Da Dumi-Dumi: Ɗan Takarar APC Ya Lashe Zaben Gwamnan Jihar Sakkwato

Da Dumi-Dumi: Ɗan Takarar APC Ya Lashe Zaben Gwamnan Jihar Sakkwato

March 20, 2023
Gwamna Umahi Ya Kori Wasu Mataimakansa Sa’o’i 48 Bayan Kammala Zabe
Labarai

Gwamna Umahi Ya Kori Wasu Mataimakansa Sa’o’i 48 Bayan Kammala Zabe

March 20, 2023
INEC Ta Bayyana Wanda Ya Lashe Zaben Gwamna A Jihar Filato
Labarai

INEC Ta Bayyana Wanda Ya Lashe Zaben Gwamna A Jihar Filato

March 20, 2023
PDP Ta Lashe Kujeru 28 Na Majalisar Dokoki, Yayin Da APC Ta Tsira Da Hudu
Labarai

PDP Ta Lashe Kujeru 28 Na Majalisar Dokoki, Yayin Da APC Ta Tsira Da Hudu

March 20, 2023
Gwamna Umahi Ya Kori Wasu Mataimakansa Sa’o’i 48 Bayan Kammala Zabe

Gwamna Umahi Ya Kori Wasu Mataimakansa Sa’o’i 48 Bayan Kammala Zabe

March 20, 2023
INEC Ta Bayyana Wanda Ya Lashe Zaben Gwamna A Jihar Filato

INEC Ta Bayyana Wanda Ya Lashe Zaben Gwamna A Jihar Filato

March 20, 2023
PDP Ta Lashe Kujeru 28 Na Majalisar Dokoki, Yayin Da APC Ta Tsira Da Hudu

PDP Ta Lashe Kujeru 28 Na Majalisar Dokoki, Yayin Da APC Ta Tsira Da Hudu

March 20, 2023

Twitter

Archives

Recent Posts

  • Gwamna Umahi Ya Kori Wasu Mataimakansa Sa’o’i 48 Bayan Kammala Zabe
  • INEC Ta Bayyana Wanda Ya Lashe Zaben Gwamna A Jihar Filato
  • PDP Ta Lashe Kujeru 28 Na Majalisar Dokoki, Yayin Da APC Ta Tsira Da Hudu

Quick Links

  • Tsaro
  • Siyasa
  • Labarai
  • Wasanni
  • Kasuwanci
  • Rikicin Duniya

Contact Us

info@dimokuradiyya.com.ng

0809 912 4425 +234 809 912 4425

No. 218 Mogadishu layout Kaduna City Center Ahmadu Bello way kaduna. Kaduna, Nigeria 800273

Copyright © 2022 Dimokuradiyya Media Services LTD.

No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Rahotanni
  • Wasanni
  • Rikicin Duniya
  • Nishadi
  • More
    • Kasashen Ketare
    • Kiwon Lafiya
    • Ilimi
    • Kasuwanci
    • Noma Da Kiwo
    • Labarun Mako
    • Talla
    • Masarautu
    • Babu Maraya
    • Addini
      • Wa’azin Kirista
    • Girke-Girke
    • Waiwaye
    • Marubutanmu
    • Wasiku
    • Ni’ima Dai Mata
    • Tsaro
    • Bidiyo
    • Audio

Copyright © 2022 Dimokuradiyya Media Services LTD.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In