Wata tawagar jami’an tsaro na hadin gwiwa daga Najeriya sun hadu da takwarorinsu daga Jamhuriyar Nijar a Dakana na kasar Nijar domin tattauna yadda za su inganta tsaro a kan iyakan kasashensu da niyyar magance ‘yan bindiga.
Tawagar jami’an tsaron daga Sokoto sun hada da Jami’an sojojin Najeriya, ‘Yan sandan Najeriya, ‘Yan sandan farar hula, DSS, Jami’an Immigration, Jami’an Kwastam da kuma Jami’an hukumar tsaro ta NSCDC. Mukadashin mataimakin jami’in hulda da jama’a na sojojin Najeriya, Kwanel Sagir Musa ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar jiya Juma’a a Sokoto inda ya ce: “Wakilan Najeriya sun tattauna da takwarorinsu na Nijar kan hanyoyin da za su bi domin tunkarar kallubalen tsaro a jihar Sokoto da kewaye.”
Ya ce barazanar tsaron da ake samu a kan iyakan Najeriya da Jamhuriyar Nijar ne ya yi sanadiyar kafa tawagar hadin gwiwa na sojoji da ke sintiri a kan iyakokin kasar a Satumban 2018. Ya cigaba da cewa Brig. Janar LKN Udeagbala ne ya wakilci kwamandan Division 8, Brigade 1 na dakarun Sojojin Najeriya wanda ya jagoranci tawagar ta Najeriya a wurin taron inganta tsaron.
Source: Twitter