Cibiyar Kula da Cututtuka masu yaduwa ta Najeriya (NCDC) ta bayyana cewa an samu karin mutum uku da cutar Korona ta kashe, a yayin da aka samu sabbin mutum 477 da cutar ta kama a jihohi 17 ciki harda Birnin Tarayya Abuja a ranar Juma’a.
NCDC ta ce a cikin rahotonta da ta bayar a ranar Asabar cewa sabbin masu dauke da cutar 477 sun kawo adadin masu kamuwa da cutar a duk fadin kasar zuwa 203,991.
Sabon adadi ya daga adadin masu kamuwa da cutar da 44 a cikin awanni 24 idan aka kwatanta da wadanda suka kamu mutum 433 a ranar Alhamis.
Hukumar NCDC ta bayyana cewa jihar Legas ce ta jagoranci jadawalin kamuwa da cutar, inda ta yi samu mutane 113 dauke da cutar a yayin da ta doke jihar Ribas, wanda ta samu mutane 79. FCT kuma tana da mutum 68.
Jihar Kaduna tana da mutum 29 a ranar Alhamis, kuma mutum 39 sun kamu da cutar a ranar Juma’a. Delta (37), Abia (36), Oyo (16), Benue (12), Akwa Ibom (9), Filato (9), Cross River (7), Edo (6), Ekiti (6), Katsina (4) ), Jigawa (3), Bayelsa (2), Ogun (1), da Yobe (1).
Jihohin Nasarawa, Ondo, Osun da Sakkwato ba su sami sabon masu dauke da cutar ba.
Tun farkon barkewar cutar a watan Fabrairun 2020, Najeriya ta sami adadin mutane 203,991 daga mutane miliyan uku da aka gwada zuwa yanzu.
NCDC ta bayyana cewa daga cikin wadanda aka tabbatar sun kamu da cutar, 192,139 an sallame su daga asibiti bayan sun murmure, yayin da har yanzu akwai sama da mutane 9,172 masu dauke da cutar.
Adadin wadanda suka mutu daga COVID-19 a duk fadin kasar ya kai 2,671 har zuwa ranar Juma’a, in ji NCDC.
Ya kara da cewa Cibiyar Ayyuka ta Gaggawa ta kasa da kasa (EOC) tana ci gaba da daidaita ayyukan mayar da martani baki daya.
Najeriya ta saya kuma ta kuma ba da gudummawar alluran rigakafi daga Burtaniya, Amurka, Indiya da COVAX wata hukumar ƙasashe da yawa.