By Abbas Yakubu Yaura
Ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola, ya ce akalla rayuka da dukiyoyi 136 da kudinsu ya kai Naira tiriliyan 3 ne aka yi a sarar a tashin gobara daban-daban a fadin kasar nan a shekarar 2021.
Ya kara da cewa Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya ta ceci kadarorin da kudinsu ya kai Naira Tiriliyan 18.9, yayin da a kalla mutane 587 suka mutu tare da ceto mutane 260 daga gobarar bara.
Aregbesola, ya bayyana hakan ne a lokacin bikin kawata sabbin mataimakan kwanturololi na hukumar a Abuja ranar Alhamis.
Ya ce aikin ya sami jimillar kiran waya 2,845 na damuwa.
Wadannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai baiwa minista shawara kan harkokin yada labarai, Sola Fasure ya fitar.
A wani bangare na labarin, “A bara, FSS ta amsa kiraye-kirayen damuwa 2,845 na SOS inda aka yi asarar rayuka 136 da dukiyoyi na Naira tiriliyan 3.
“Amma hukumar FSS ta yi nasarar tserar da rayuka 587, ta ceto mutane 260 da kuma ceto dukiyoyin da suka kai Naira tiriliyan 18.9.
“A takaice dai, hannun jarin FSS ya karu matuka saboda hukumar ta bayar da gudunmawa sosai ga tsaron kasa – wajen kare rayuka da dukiyoyi,” .
Aregbesola ya bayyana cewa a tsakanin shekarar 2015 zuwa yanzu, gwamnatin tarayya karkashin jagorancin Muhammadu Buhari ta kashe kudi fiye da yadda aka kirkiro ta a shekarar 1901.
“Mai da hankali kan kare dukiyar da gwamnatin Buhari ta bayar tun daga shekarar 2015 ya fi duk abin da aka sanya a cikinta tun lokacin da aka kafa ta a shekarar 1901. Tsakanin shekarar 2015 zuwa 2020, Gwamnatin Tarayya ta samar da motocin kashe gobara na zamani 106 ga hukumar ta FSS.
“A shekarar da ta gabata, Majalisar Zartarwa ta Tarayya ta amince (tun daga lokacin da aka sayo aka tura ta) inganta ayyukan more rayuwa na Naira biliyan 10.4 da suka hada da injunan kashe gobara 44, da tankunan ruwa 15, injinan kashe gobara 15 cikin gaggawa (ba na al’ada ba) da za su iya shiga cikin wannan fanni.Har ila yau, an aika da jami’an kashe gobara 17 zuwa kasar Belarus domin daukar horon karin kwarewar aiki.
Wadannan jami’an su ne kwararrun da za su horas da sauran jami’an kan yadda zasu kashe gobara da kayan aiki na zamani, bala’i da kuma kula da gaggawa.”