By Abbas Yakubu Yaura
Gwamnan jihar Imo, Sanata Hope Uzodimma, ya ce nan da makonni biyu zai bayyana wadanda ke daukar nauyin kashe-kashe a jihar sa.
Da yake zantawa da ‘yan jarida a Legas, Uzodimma ya dage cewa ya gano ‘yan siyasar da ke haddasa rashin tsaro a jihar, kuma jami’an tsaro suna ci gaba da bincike kan lamarin.
Ya ce, “’yan siyasa da ke adawa da jam’iyyar APC ne ke da hannu wajen kashe-kashe da nakasa jihar, kuma na sha alwashin bayyana sunayensu. Sai dai na yi wata ganawa da jami’an tsaro wadanda suka roki cewa bayyana sunayen wadanda suke daukar nauyin lamarin, gudanar da bincike na iya kawo cikas ga yunkurin.
“Lokacin karshe da na tuntube su kwanakin baya, sun bukaci karin makonni biyu. Ina fatan nan da makonni biyu za a shirya rahoton sannan kuma a bayyana shi ga ‘yan Najeriya.”
Gwamnan ya kuma yi magana kan neman shugabancin yankin Kudu maso Gabas, inda ya bayyana cewa shugabancin Igbo a 2023 zai magance rashin adalci da kuma nuna kukan wariyar launin fata a yankin.
“Kowace jam’iyyar siyasa tana bayan karfin ‘yan takara don cin zabe. A Kudu-maso-Gabas, a shirye muke mu fitar da Shugaban Najeriya. Akwai tausayin kasa ga Kudu maso Gabas don samar da Shugaban kasa.
Abin da zai sanya shi aiki shi ne manyan jam’iyyun siyasa biyu su fitar da ‘yan takara daga shiyyar Kudu-maso-Gabas.
“Bari jam’iyyar PDP ta fitar da dan kudu maso gabas a matsayin dan takarar shugaban kasa. Su ma APC su fitar da dan Kudu maso Gabas a matsayin dan takararsu na shugaban kasa. Da wannan ne, za mu mayar da wannan rabon mulki ta yadda ya zama gama gari da gaskiya da adalci,” ya kara da cewa.
Comments 1