• Wata kungiya ce ta bukaci gwamnan ya tsaya takaran Shugabancin kasar nan a zaben shekarar 2023 mai zuwa.
• “Nan da mako uku zan yanke matsaya na dangane da wannan batu” inji Gwamnan.
•Na kanyi komai bisa yaddar Allah ne.
Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya bukaci kungiyoyi siyaya da kungiyar shugabannin matasa na yankin Arewa NYLF, da su ba shi, nan da mako uku, domin ya yanke shawaran fidda matsayar shi, dangane da tsaya war shi takaran Shugabancin kasar nan a shekarar 2023
Gwamnan ya bukaci haka ne a jiya laraba, lokacin da kungiyar ta gabatar mai da takardar bukatar tsayawar shi takaran Shugaban kasa, a babban zabe me zuwa.
Mambobin zartarwa ta kungiyar NYLF, Wanda Shugaban ta na Kasa, Elliot Afiyi ya jagoran ta, sun gana da gwamnan ne a dakin taro Banquet, da ke gidan gwamnatin jihar.
KARANTA WANNAN LABARIN: Mutun uku da su ke juya masana’antar Kannywood
Inda Gwamnan ya ce, “Bazan iya bako amsa ba a yanzu, har sai na tuntubi wasu yan siyasa daga jam’iya, kafin daga bisani na bayyana matsaya na.”
Inda ya Kara da cewa, ” Ina gudanar da komai ne, bisa yaddar Allah, don haka kubani nan da mako biyu zuwa uku, domin yanke matsaya na, na karshe kan wannan batu.” inji gwamnan jihar.
Comments 1