Daga: Abbas Yakubu Yaura
Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce nan da watanni shida ‘yan Najeriya za su yaba wa gwamnatin jam’iyyar APC bisa ba su ‘yancin kada kuri’ar da suka zaba.
Buhari ya bayyana haka ne a ranar Talata a lokacin da ya karbi bakuncin mambobin kungiyar gwamnonin APC, PGF karkashin jagorancin shugaban kuma gwamnan jihar Kebbi, Abubakar Atiku Bagudu, a fadar gwamnati da ke Abuja.
KARANTA WANNAN LABARIN; Ganduje Ya Dakatar Da Rantsar Da Sabbin Kwamishinonin Biyo Bayan Rugujewar Gini, Ambaliya
Shugaban ya ce gwamnatinsa ba za ta bari a tsorata ‘yan Najeriya a zaben 2023 ba.
Ya ce, “Ba za mu yarda kowa ya yi amfani da dukiyarsa ko kuma tasirinsa wajen tsoratar da wasu ‘yan Najeriya ba.”
“Ba za mu ƙyale tsoratarwa ta zahiri da ɗabi’a ba. Wannan shi ne irin shugabancin da zai iya fitowa ya kuma tabbatar da al’ummarmu.”
“Nan da watanni shida, ‘yan Najeriya za su yaba da gwamnatin APC da cewa muna da gaskiya kuma muna girmama su.”
A cewar wata sanarwa da mai magana da yawunsa Femi Adesina ya fitar, Buhari ya bayyana cewa rashin tsoma baki a zabe yana tabbatar da tsarin siyasa da tabbatar da shiga da kuma hada kai.
Da yake tsokaci kan zabukan gwamnoni da aka gudanar a jihohin Ekiti, Anambra da Osun, Buhari ya ba da tabbacin cewa APC za ta ci gaba da tabbatar da cewa zaben ya nuna zabin al’ummar kasar.
“Ina so ’yan Najeriya su sani cewa muna girmama su, kuma mun nuna cewa za mu ba su damar zaben wanda suke so. Duk mun shaida abin da ya faru a jihohin Anambra, Ekiti da Osun. Abin da ya faru a waɗannan jihohin ya ba ni fata mai yawa cewa muna samun nasara.”
Buhari ya kuma bukaci shugabannin jam’iyyar APC da su rubanya kokarinsu wajen yin tunani da dabarun tunkarar zaben 2023 mai zuwa.
Goyon bayan ku zai karfafa aikin jarida a Najeriya kuma zai taimaka wa dimokuradiyyar mu.
A wani labarin kuma Gwamnatin Enugu Ta Rufe Makarantu Masu Zaman Kansu
Gwamnatin jihar Enugu ta bayar da umarnin rufe dukkan makarantu masu zaman kansu a matakin farko da ke aiki a jihar ba tare da amincewar ma’aikatar ilimi ta jihar ba a rubuce.
Umurnin, a cewar kwamishinan ilimi Farfesa Uche Eze, ya kasance a ci gaba da bunkasar makarantu masu zaman kansu marasa inganci a jihar Enugu ba tare da neman rajista ko samun amincewar ma’aikatar kamar yadda doka ta tanada ba.