By Abbas Yakubu Yaura
Wata kotu a garin Lafia ta yanke wa wasu mutane 48 hukuncin daurin watanni shida a gidan yari bisa samunsu da laifin karya dokar tsaftace muhalli ta jihar Nasarawa.
Kotun ta tafi da gidanka, ta baiwa wadanda aka yanke wa hukuncin laifin zabin biyan tarar Naira 5,000 zuwa Naira dubu 50,000 a zamanta na ranar Asabar.
Dan sanda mai gabatar da kara, Abubakar Mohammed, wanda kuma babban jami’in kula da muhalli ne a jihar, ya shaida wa kotun cewa wadanda ake zargin suna yin mu’amala da sana’o’insu na kashin kansu, yayin da ake ci gaba da aikin tsaftace muhalli na wata-wata, inda Mista Mohammed ya ce laifin ya saba wa dokar muhalli ta jihar.
Sannan ya bukaci kotun data sanya wa masu laifin takunkumi domin su zama izina ga sauran masu son yin laifin anan gaba.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa Alkalin kotun, Abdullahi Lande, ya yanke wa mutane 48 hukuncin daya dace dasu.
A halin da ake ciki, babban sakataren ma’aikatar muhalli da albarkatun kasa, Aliyu Agwai, ya yabawa sauran mazauna jihar bisa bin dokar tsaftar muhalli.Mista Agwai ya ce an toshe hanyoyin shiga jihar ne yayin da ake gudanar da atisayen domin hana zirga-zirgar ababen hawa daga wajen jihar.
Kazalika yace “Mun ba da izinin zirga zirgar ababan hawa daga ma’aikatun da suka dace, ko kuma waɗanda ke kan muhimman ayyuka su wuce su zagaya yayin atisayen,” in ji shi.Ya kuma yi kira ga al’umma da su rika tsaftace muhallinsu a koda yaushe domin gujewa barkewar cututtuka.
“Akarshe yace ya kamata mazauna yankin su kara baiwa gwamnati hadin kai domin amfanin kansu don ganin jihar ta kasance cikin tsafta.sannan Gwamnatin jihar Nasarawa ta kebe ranar Asabar ta karshen kowane wata domin aikin tsaftar muhalli.