Jam’iyyar PDP reshen jihar Nasarawa, ta sake sanya ranar yakin neman zaben ta kafin zaben 2023, biyo bayan rashin amincewa da ‘yan sanda suka yi.
Jam’iyyar ta tsayar da ranar Litinin 28 ga watan Nuwamba domin fara yakin neman zabe a karamar hukumar Toto, amma sai ta samu canjin rana zuwa Talata 29 ga watan Nuwamba 2022.
KARANTA WANNAN LABARIN: Kotu Ta Kori Dan Takarar Gwamnan ADC Da Na Majalisar Dokokin Jihar Ogun
Mista Francis Orogu, shugaban jam’iyyar a jihar, ya tabbatar da hakan a wani taron manema labarai ranar Juma’a a karamar hukumar Karu.
Ya ce jam’iyyar ta nemi kuma ta samu amincewar ‘yan sanda don gudanar da taron a ranar 28 ga watan Nuwamba a karamar hukumar Toto.
Orogu, ya ce yayin da ake shirin gudanar da taron, jam’iyyar ta samu takarda daga kwamishinan ‘yan sanda, Maiyaki Mohammed-Baba a ranar Juma’a, 25 ga watan Nuwamba, cewa ba za a bari a gudanar da taron ba.
“Shi (CP) ya ce shugaban karamar hukumar Toto ne ya sanar da shi cewa bai san zuwanmu ba.
“Wannan abin abin dariya ne, kuma a gare mu muguwa ce ta hanyar dimokuradiyya domin mun san cewa Kwamishinan ‘yan sanda ya san cewa shugaban karamar hukuma ba shi da sarari a karkashin dokar zabe da za a sanar da shi tare da ba da izinin yin yakin neman zabe a karamar hukumarsa,” in ji Orogu.
Ya yi ikirarin cewa jam’iyyar PDP ce ta fara bayyana jadawalin yakin neman zabenta kuma yana mamakin dalilin da ya sa jam’iyyar APC ke dagewa za su fara yakin neman zaben daga karamar hukuma daya kuma arana guda.
Shugaban ya kara da cewa tun da farko PDP ta tsayar da ranar 26 ga watan Nuwamba domin fara yakin neman zabe a jihar amma sai suka ji an ce APC za ta fara yakin neman zabe a ranar 28 ga watan Nuwamba. Hakanan ba zai yiwu ba bayan kashe kayan aiki da lokaci don shirya taron.”
Shima da yake magana, Mista Labaran Maku, Darakta-Janar na kwamitin Yakin Neman Zaben PDP ya bayyana matukar takaicin wannan ci gaban da aka samu tare da yin kira da a tsai da kuduri daga hukumomin tsaro.
“Abin mamaki ne a sa’o’i 48 suka rage mu je gangamin yakin neman zabenmu, kwatsam mun samu wannan wasika duk da cewa jam’iyyarmu ce ta fara sanar da ‘yan sanda jadawalin yakin neman zabenmu,” inji shi.
Maku ya ce bayan tuntubar shugabannin jam’iyyar da kuma majalisar kamfen din sun amince da sauya rana da tutar jam’iyyar a karamar hukumar Toto zuwa ranar 29 ga watan Nuwamba.
“Muna baiwa rundunar ‘yan sandan Najeriya tabbacin cewa muna bin doka da oda amma muna fata ba za’a rushe sauran jadawalin ba.
Da yake mayar da martani, DSP Ramhan Nansel, jami’in hulda da jama’a na ‘yan sandan jihar Nasarawa, ya karyata zargin da suka yi na cewa ‘yan sandan sun umarci jam’iyyar PDP da ta dakatar da shirin yakin neman zabenta a karamar hukumar Toto a ranar 28 ga watan Nuwamba.
Ya ce an samu sabani na kwanan wata da wuri da APC da CP Mohammed-Baba, sai dai ya shawarci jam’iyyar PDP da ta canja taronta zuwa washegari domin a dakile rikici tsakanin magoya bayansu, da kuma samar da isasshen tsaro ga bangarorin biyun a yayin gangamin yakin neman zabe.
“Don haka, saboda samar da isasshen tsaro ga jam’iyyun siyasa biyu ne ‘yan sanda suka shawarci PDP da su sauya nasu zuwa washe gari. Ba wai kai tsaye aka tsayar da su ba ko kuma aka hana su ba,” inji shi.NAN
A wani labarin kuma, Sanata Uba Sani Ya Yi Allah-Wadai Da Kashe-kashen Kananan Hukumomi Uku Na Jihar Kaduna
Dan takarar gwamnan jihar Kaduna a karkashin jam’iyyar APC Sanata Uba Sani, ya yi Allah-wadai da hare-haren wuce gona da iri da kuma lalata rayuka da dukiyoyi a kananan hukumomin Giwa, Birnin Gwari da Kajuru na jihar da wasu ‘yan bindiga suka yi.
Ya yi Allah-wadai da hakan ne a ranar Juma’a ta shafinsa na Facebook, inda ya ce dole ne hukumomin tsaro su yi kasa a gwiwa wajen gurfanar da masu aikata miyagun laifuka a gaban kotu.
“Labarin kashe-kashen da aka yi a kananan hukumomin Giwa, Birnin Gwari da Kajuru abin bakin ciki ne kuma ina tare da Gwamna Nasir El-Rufai wajen mika ta’aziyyata ga wadanda suka rasa ‘yan uwansu a irin wannan mummunan lamari.”