Jami’an hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA, sun kama tubalai 22 na tabar heroin masu nauyin kilogiram 23.55 da aka boye a cikin kwanikan abincin jarirai Nestle Cerelac a filin jirgin sama na Murtala Muhammed International (MMIA), da ke Ikeja, a Legas.
A wata sanarwa da hukumar ta NDLEA ta fitar a ranar Lahadin nan, ta bayyana cewa, kayayyakin da darajarsu ta kai sama da Naira biliyan 4.5 ta fito ne daga birnin Johannesburg na kasar Afirka ta Kudu a cikin jirgin South African Airways a ranar Laraba 29 ga watan Yuni a wani bangare na hadakar da ta isa wurin shigo da kaya na SAHCO. filin jirgin saman Legas.
Bayan wasu jerin ayyukan bibiyar lamarin da ya kai ga kama wasu jami’an jigilar kaya biyu, an kama ainihin mai karbar kwayoyin, Chike Okeke Eweni wanda ke rarraba wa abokin aikin sa na Afirka ta Kudu kayan washegari, Alhamis 30 ga watan Yuni a wani kantin sayar da kayayyaki, a Ajao Estate, dake Ikeja. Chike wanda ya fito daga karamar hukumar Anaocha, jihar Anambra ya yi ikirari yayin wata tattaunawa ta farko cewa shi ma yana kiyon kifi.
Kafin kama Chike, jami’an NDLEA a filin jirgin saman sun kama wani tsohon direban kamfanin sufurin jama’a, BRT, Muyiwa Babalola Bolujoko a ranar Litinin 27 ga watan Yuni da laifin shan kwaya 90 na hodar iblis. An kama shi ne a wurin da ake tantance shi kafin ya hau jirgin Qatar Airways da ke kan hanyar Doha zuwa Sharjah, inda ake sa ran tafiyar tasa za ta kare a birnin Dubai na kasar Hadaddiyar Daular Larabawa.
Matashin mai shekaru 39 daga karamar hukumar Ijebu ta Kudu, jihar Ogun, an sanya masa ido ne bayan da sakamakon binciken jikin sa ya tabbatar da shan miyagun kwayoyi. A yayin da ake tsare da wanda ake zargin, ya fitar da dukkanin pellet din guda 90 a cikin najasa hudu.
Ya yi ikirarin cewa ya bar aikin da yake yi na N60,000 a duk wata a matsayin direban BRT a watan Fabrairu kuma ya yanke shawarar yin aiki a matsayin mai jigilar kwayoyi don samun kudi don siyan motar bus din da aka fi sani da ‘Korope’ a Legas don ci gaba da sana’ar sufuri.
Har ila yau, a ranar Alhamis 30 ga watan Yuni, jami’an tsaro sun kama wani dandali na ganyen kati da ke shigowa, wanda ya isa rumfar shigo da kaya NAHCO na filin jirgin saman Legas a jirgin Royal Air Maroc daga Gabas ta Tsakiya. An gano busasshen ganyen katon guda 71 mai nauyin kilogiram 2,434.3 a cikin kayan.
Hakazalika, jami’an hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi na hukumar a ranar Alhamis din da ta gabata sun kama wasu nau’ikan tabar wiwi guda 36 na jihar Colorado, wani nau’in tabar wiwi mai nauyin kilogiram 19.30 wanda ya isa rumfar da NAHCO ta shigo da su daga birnin Los Angeles na kasar Amurka a cikin jirgin Delta Airlines.
Dimokuradiyya ta rawaito cewa, Bayan gudanar da wani bincike da aka yi inda aka kama mutane hudu, a karshe an kama ainihin mamallakin maganin, Abibu Afis Sola a ranar Juma’a 1 ga watan Yuli a unguwar Gbagada da ke Legas.
A halin yanzu, a jihar Ribas, jami’an NDLEA a ranar Laraba 29 ga watan Yuni sun kama wata mata mai shekaru 68 mai suna Misis Celina Ekeke a unguwar Obunku, da ke karamar hukumar Oyigbo da tabar wiwi kilogiram 231.2, yayin da Shedrack Eze daya aka kama washegari Alhamis 30 ga watan Yuni. Yankarfe, Zaria, da ke Kaduna dauke da alluran Exol 5 250,000, nauyin kilogiram 75. A jihar Borno, an kama Usman Haruna mai shekaru 27 a shingen bincike na BCG da ke Biu a ranar Asabar 2 ga watan Yuli da tabar wiwi mai nauyin kilogiram 19.7.
Shugaban Hukumar NDLEA, Burgediya Janar Mohamed Buba Marwa (Mai Ritaya) ya bayyana jin dadinsa da yadda da jami’an rundunar MMIA suka yi kyakkyawan aiki a cikin makon da ya gabata yayin da ya kuma yabawa na Ribas da Kaduna da kuma Borno da suka yi taka tsantsan. Ya bukace su da sauran su a duk fadin kasar da su ci gaba da daukar matakai gabanin yaudarar ‘yan kungiyar masu fataucin miyagun kwayoyi.