Rundunar hukumar hana sha da fataucin kwayoyi ta kasa wato NDLEA ta yi babban kamu a jihar Taraba, inda ta kama mutum 25 da ake zargi da dillancin kwayoyi a Jihar.
Kwamandan rundunar ta NDLEA da ke jihar, Alhaji Suleiman Jadi, ya ce wadanda ake zargin an kama su ne tare da tulin kwayoyi a inda suke, wanda hakan ya tabbatar da zargin da ake musu.
Suleiman Jadi ya bayyana cewa abubuwan da aka kwace sun hada da Kwayar Cannibas Sativa mai Nauyin Kilogiram 239.9 da kuma Psychotropic Mai nauyin kilogoram 59.7 gami da kwalabe 274 na syrinps da codeine.
Alhaji Jadi ya bayyana cewa tara daga cikin wadanda ake tuhumar an gurfanar da su a babbar kotun tarayya da ke Jalingo yayin da ake ci gaba da bincike kan ragowar wadanda ake zargin