Ni ba sa anka bane a Siyasa– Dogara ya yi Zazzafan martani ga q Keyamo
Tsohon Kakakin Majalisar Wakilai, Yakubu Dogara, ya mayar da martani game da yadda Festus Keyamo ya bayyana shi a matsayin “mai karuwancin siyasa kuma mai cin mutuncin mutane.”
Dogara ya ce shi ma yana da sunan da bai dace da Keyamo ba.
KARANTA WANNAN LABARIN:Yan Najeriya Na Bukatar Mako 2 Don Su Murmured Bayan Saukar Buhari – Kato
Bayanin nasa na kunshe ne a wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter ranar Lahadi.
Idan za’a tuna cewa Keyamo, Karamin Ministan Kwadago da Aiki, kuma mai magana da yawun kwamitin yakin neman zaben Tinubu-Shettima, ya bayyana a shafinsa na Twitter a safiyar Lahadin da ta gabata, inda ya kira Dogara a matsayin “Karuwan siyasa, mai cin mutuncin mutane.”
Keyamo na mayar da martani ne kan kalaman Dogara inda ya yi nuni da goyon bayan da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi wa Bola Tinubu, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a yakin neman zabe a jihar Nasarawa, a matsayin abin dariya.
Keyamo ya rubuta: “Yayana kuma abokin karatuna, @YakubDogara, wannan tweet yana ƙarƙashinka. Haƙiƙa kuna jin daɗin goyon bayan PMB na @officialABAT, shugabanni biyu waɗanda suka tsaya kan aƙidarsu da manufofinsu, ba kamar karuwan siyasa ba, mai yawo da ƴan daba da kuka kasance koyaushe.”
Duk da haka, Dogara ya mayar wa Keyamo martani: “Yayana, ina da suna a gare ka amma saboda ba shi da kyau, ba zan fadi hakan a matsayin kudin abota ba. Eh, mun kasance mataye a Makarantar Lauyoyi amma ina jiran ku da ku fara cin zaben kansila domin mu zama abokan zama a siyasa. Koyi naushi ƙasa da nau’in nauyin ku.
A wani labarin kuma: Manchester United Ta Taya Ronaldo Murnar Zagayowar Ranar Haihuwar Sa
Manchester United ta aike da sako ga Cristiano Ronaldo a ranar da yake bikin cika shekaru 38 da haihuwa.
Kungiyar ta Red Devil ta wallafa sakon taya murna ga dan wasan na Portugal a shafukan sada zumunta.