A cewar sa Gwamnan Jihar zamfara Abdul’aziz yari Abubakar, a jiya ranar ma’aikata yace shi zai zama na farko wajen biyan sabon albahshi.
Yayi da yake bayani a gun taron Yari, yayi kira ga ma’aikata da su daina saka matan su da ‘ya’yansu cikin wadanda ake biya.
Wanda ya samu wakilcin sakataren Gwamnati. Farfesa Abdullahi Muhammad Shinkafi, yace bai kamata ‘ya’yan ma’aiktan suna shiga tsarin wadanda ake Biya ba, wannan ke kawo rashin dai dai to ga Al’umma.
Yace zai biya duk hakkin su kafin barin shi Karagar Mulki, Shugaban Kwadago na jahar Bashir mafara yayi kira ga Gwamnati da ta cika duk alkawuran da ta dauka ya yin yakin Neman Zabe.