Tare Da Sulaiman Umar AC
Wani dan tasi ne ya dauko yara daga makaranta, sai wani daga cikinsu ya yi ta surutu, yana karatun da aka koya masu a ranar, yana cewa: “Idan babana sarki ne, mamata sarauniya, zan zama yarima.” dan tasi ya damu kwarai,
sai ya ce wa yaron: “Idan babanka dan fashi ne fa, kuma innarka karuwa, kai kuma me za ka zama?” Sai (yaro) ya ce: “Sai in zama dan tasi kamarka!”